5-6

1.6K 120 6
                                    


_*MARUBUTA* masu rubuta littattafan kuɗi wanda suke buƙata ai masu tallah domin su ƙara samun costumer zasu iya nemana domin a tallata masu littafansu cikin sauƙi da kwanciyar hankali🤗_ _*MAKARANTA* wanda suke business kuma suke buƙatar a tallata masu hajarsu suma zasu iya nema ta wannan number 08119237616 zan baza maka tallan business ɗinka zuwa wajaje da dama inda zaka samu costumer siyan ɗaiɗai ko sari 😇_

Wattpad Nimcyluv



Girgiza masa kayi tayi ba tare data ƙara magana ba tayi lamo a jikinsa,turo da yatsan daya sa mata a baki tayi,kafun ta kallesa taga ya rufe idanunsa yana bacci,hannunta tasa ta shafi sajensa tace "laaaa Dad kaima kana da irin na Dad na" shuru yayi mata bawai dan baya jinta ba,lips ɗinsa ta taɓa ta ƙara faɗin "Dad kaima kana shan sweet ne" kafin ta ƙara faɗin wani abun aka fara bugun ƙofar ƙaramin ɗakin nasa,da sauri ya miƙe tsaye  tare da ɗaukan Moon ya sanyata a bayan ƙofa, buɗe ƙofar yayi ganin Alhaji  tsaye yasa yayi shuru yana kallonsa kafin yace "mrng Alhaji" Alhaji yace "mrng too ba zaka fito ai jana'izar da kai bane?" Ƙasa yayi da kansa sbd kallon da yaga Alhajin nayi masa gaba ɗaya ya manta cewa gashin kansa a kunce yake,cikin basarwa yace "eh,ban jin daɗi ne" jinjina kai Alhaji yayi alamar gamsuwa kafin ya juya ya nufi cikin motarsa yayi waje,yana zuwa ya fito daga motar ya karasa wajan jami'in jana'izar da za'ai,gaba aka shimfiɗesu su uku har yanzu jini bai bar zuba daga cikin ko wannan su ba, addu'ar da ake yi a cikin sallar jana'iza Liman ɗin ya fara.
"اللهم اغفر لله وارحمه،وعاعف عنه،وأكرم نزاله،ووسع مدخله،واغسله بالماء والثج والبرد،ونقه من الطايا كما نقيت الصوب الأبيض من الدنس،وأبدله دآرآ خير من داره،وأهلا خيرآ من زوجه وأدخله الجنة،وأعذه من عذاب القبر وعذاب النار."
_(Ya Allah ka yi masa gafara,ka jiƙansa,ka amintar da shi daga bala'i ka yi masa rangwame,kuma ka girmama liyafarsa,ka yalwata mashigarsa (kabarinsa), kuma ka wanke laifukansa kamar yadda ka ke tsaftace farar tura daga dauɗa, kuma ka musanya masa gidan da ya fi gidansa alheri,da mutanen gida da suka fi mutanen gidansa alheri,da mata matar da ta fi matarsa alheri (da mijin daya fi mijinta alheri) kuma ga shigar da shi /ita aljanna,ka tserar ta da shi /ita daga azabar kabari da azabar wuta)_

Ana kammala jana'izar aka miƙa su zuwa gidansu na gsy,bayan an dawo Alhaji yana zaune a saman danning yana breakfast gefensa Farouk da Yasmin sai matarsa Hajja khadu suna kiranta da Ummi ta kallesa tace "wannan lamarin yana bani mamaki,ace an kashe kowa na gidan amma a rasa inda ƙaramar yarinya take,wannan wacce irin rayuwace yanzu wa yasan halin da yarinyar take ciki, Allah yana gani da za'a ga rinyar nan nice zan riƙe ta,Alhaji anya ba wanda suka aikata wannan abin bane suka ɗauke ta ba?" Ta faɗa tana ɗaukan tea tare da kaiwa bakinta Farouk yace "Ummi ko ajiya naga yarinyar ta tsallako titi hannunta riƙe da ice cream,sosai nai mmki sbd ban taɓa tunanin aƙwai wata ƙaramar yarinya ba a cikin gidan" Ummi tace "Nima sau ɗaya na taɓa ganinta,kamar dai basa barinta fita tunda ko compound na gidan da wahala ka ganta ciki" sai lokacin Yasmin tace "to Ummi ko dai ɓoyeta suke?" Kai Alhaji ya ɗaga ya kalli autar tasa kafin ya miƙe yace "Auta me zai sanya a ɓoye ƴar ne? Kawai da bata da cikakkiyar lafiya shiyasa ko da wanne lokaci a kuma ko ina ciwonta na iya tashi"yana faɗin hakan yay shuru da bakinsa ya nufi part ɗinsa, cikin ƙasa da murya Farouk yace "Ummi meke damunta?" Miƙewa Ummi tayi tace "Ni tayaya zan sanan wannan lamari Allah dai ya bai yana ta,ko kuma ya kaita hannu na gari, Allah sarki ƙyakkyawar yarinya da ita"

Ummi ta faɗa tana miƙewa tsaye tare da kiran sunan mai aikinta Hanne,Hanne na zuwa tace "gani Hajiya" Ummi tace "yawwa Hanne ɗauki warmer ɗin nan ki miƙa wa mai gadi nasa breakfast ɗin" cikin girmamawa Hanne ta amsa tare da fice daga cikin gida...
Yana ƙwance Moon na jikinsa sai ya mutsa masa gefen fuskarsa take,fuska ta kwaɓe tace "Dad i want eat food,ina jin yunwa"sai a lokacin ya ware idanunsa wanda suka ɗan janye kaɗan yace "kee shuru" cikin muryar kuka tace "Please Dad" baya ya juya mata ba tare da yace mata komai ba,baki ta buɗe zata magana yayi saurin rufe mata bakin,a lokacin kuma aka fara buga ƙofar ɗakin miƙewa yayi tare da tura Moon bayan ƙofa,jerarrun hqranta ta buɗe tare da ɗaga hannunta ta girgiza alamar ba zatai magana ba..
Buɗe ƙofar yayi yaga Hanne tsaye hannunta riƙe da warmer, bai ce mata komai ba sai data gama kallonsa tace "abin karyawa" amsa yayi tare da juyawa da sauri tace "bawan Allah yaya mu kaji da wannan tashin hankalin ɗaya samemu yau" cikin ƙasa da Murya yace "Allahamdulillah" tace "wanann rashin imani dame yayi kama,OHHH! ni Hanne yanzu har ƴar yarinyar nan ba'a gani ba,kaii duniya ina zaki damu ko me ya tare masu ohhhu..,ai ɗazo Alhaji ya dawo daga jana'izar wai har aka saka su makwancin su jini na zuba..,Ni kam nace wanne irin harbi akai masu?" Tunda ta fara magana yake kallonta ba tare daya tan kata,ta buɗe baki zatai wata maganar yayi saurin juyawa ya barta tsaye baki a buɗe.
Wajan gate ta nufa tare da leƙawa ta wata ƙofa ta hangi gidansu Moon tace "Allahu akbar,yanzu duk girman gidan nan babu kowa,yooo duniya kenan kana zaune da kowa lfy baka san me ƙullatarka a zcy ba,mutum zcyarsa fari fattt amma ta wani tirrrr kada kasu kaga baƙin dake cikinta sbd mugun abu,yanzu wannan gidan kayan daɗi na nan kala kala kuma iri-iri karama bonvita da obalti suji lbr,ko ina marainiyar Allah tayi ohhhhu,amma dole zan bincika idan na tabbatar da abinda nake tunani babu shakka zan bata taimako wanda zai zame mata kariya irin na har abada ɗin nan"jin motsi a bayanta yasa ta juya da sauri dan ganin wanene,tsaye taga Farouk sanye da riga da wando na baƙin yadin boyal sai ƙamshi yake,ganin yana kallon ɗakin Deen yasa itama ta kalli direction ɗin da yake kallo itama, ɗauke kansa kawai yayi ya nufi wajan motarsa yabar gidan gaba ɗaya ba tare da yyiwa Deen magana ba,itama Laure juyawa ta nufi cikin gida..
Ajjiyar zcy Deen ya sauke bayan yaga Farouk ya fice daga cikin gidan, ƙaramin ribbon ya ɗauka ya naɗe gashin kansa dashi kafin ya juya ya nufi inda ya ajjiye warmer ɗin breakfast ɗin,zama yayi ya ɗan lumshe idanunsa, Moon dake zaune hannunta riƙe da teddy tace "Dad" kallonta yayi na wasu seconds kana ya ɗauke idanunsa a kanta ya zama can gefe yace "eat" Moon ta kalli warmer ɗin kana tace "Dady nane yazo ko, Dad kace masa bana nan sai na daɗe wajanka zan koma"still ƙansa yana ƙasa bai ce mata komai ba,shuru ne ya biyo baya kafin ta miƙe ta zauna daf dashi tace "Dad mene jana'iza?" Ɗan waro idanunsa yayi cike da mmki kafin ya ɗaga kai ya kalleta nan ma shuru yayi mata bai kula ta ba,marai-raice fuska tayi tace "wata rana na taɓa ji Daddy yace yaje jana'iza,amma ni ban son ai masa jana'iza" nan ma kallonta yayi kana ya ɗauke idanunsa yaci gaba da latsa babbar wayarsa mai ƙirar iphone 12 max pro, murmushi tayi masa har sai da beauty points ɗinta suka loma tace "kasan me yasa nace haka..?" tsaki yaja kafin yace "talkative..! Shut up" yana faɗin hakan yayi ƙasa da murya cikin nutsuwa yace"Ututu oma" (good morning) shuru yayi yana sauraran abinda ake faɗa masa,kafin yaja idanunsa ya lumshe idanunsa ya sauke ajjiyar zcy yace "owk" yana faɗin hakan ya kashe wayar,kana ya kunna data wayarsa ya shiga I.G yana shiga messages ɗin Nana khadii wajan biyar suka shigo cikin wayarsa wani lalataccen murmushi gefen baki yayi kafin  ya fara karanta messages ɗin kamar haka.
_na riga na faɗawa iyaye na, kuma sun amince_
Hannu yasa yaja gefenmu ya ƙara ware manyan idanunsa.
_Na jika shuru_
Messages ɗinta na huɗu ya duba.
_Allah yasa ba aikin ka fasayi dani ba_
Cikin sauri sauri ya rubuta mata "ok gobe ki sameni a *Nnamdi Azikiwe International Airport* by 10:30, za kiga wani sanye da blue ɗin  sweater You can follow him" yana gama typing ɗin yayi send kana ya kashe data na wayar,wani danne danne yayi wajan 5seconds ya kashe wayar gaba ɗaya ya ajjiye ta a ƙasa pillow, Moon da yunwa ya fara cinta tayi shuru tana kallonsa kamar mai nazartar wani abu a wajansa,sai kuma tace "Dad zan sha tea" ɗago kai yayi da sauri sbd gaba ɗaya ya manta da ita a ɗakin,inda Allah ya taimake sa ba wani abu yace ba,komai a rubuce yayi shi,dan sosai ya fahimci shegen surutun da take dashi, haɗe fuska yyi sai kuma yaja warmer ɗin ya buɗe,wajan part huɗu ne cikin warmer ɗin kafin yasa hannu ya buɗe part ɗin farko soyayyan dankalin turawa ne wanda yasha ƙwai, ɗaya part ɗin ya buɗe yaga soyayyiyar doya,fito dasu yayi tare tura mata gabanta yace "ohhyaa ci" kamar jira take tai bisimillah  ta fara cin dankali sai da ta cinye tass sannan sannan ta ture doyan tace "Dad water" fesar da numfashi ya ɗauki hularsa ya saka a kansa tare da tura duka gashinsa ciki,ya fita zuwa waje,wajan 10minutes ya dawo hannunsa riƙe da gorar ruwa mai sanyi da mara sanyi sai kuma chocolate,yana shigowa Alhaji na fitowa daga cikin gida zai fita,kallon Deen yayi yace "chocolate kamar yaro" cije lips yayi ba tare kuma da yace komai ba ya buɗe ɗakin ya shiga,tana zaune riƙe da wayarsa a kunanta da sauri ya amshe wayar,kallonsa Moon tayi tace "ance ka kai babyn wai" hannu yasa ya rankwashi tsakiyar kanta yace "kika ƙara taɓa wayar saina harbeki stupid"Baki ta buɗe zatai kuka yayi sauri jawo ta jikinsa ya rungome haɗe dasa hannu ya toshe mata bakin,da idanu kawai Alhaji yabi Deen da kallo kafin yayi murmushi ya shige cikin motarsa,shuru yayi mata yana jin yadda take tauna hannunsa da haƙoranta yay mata banza, buɗe idanunsa yayi sbd horn ɗin da yaji a nayi janye jikinsa yayi ya nufi waje,motar Alhaji ya gani a gaban gate da nutsuwar da ta gama zama a jikinsa ya buɗe gate ɗin ba tare da kalli motar ba yaja baya,shima Alhajin baiko kalli inda yake ba ya fice daga cikin gidan.
Da yamma wajan ƙarfe biyar Deen na zaune saman benci a gefen gate bayan ya lallaɓa Moon tayi bacci sbd kukan Mummy da Daddy data fara.
Daga can gefen yaji ana faɗin "  yallaɓai C.P  (commissioner of police) bawai ina tunani bane,a'a ina son na tabbatar maka yarinyar nan aƙwai wanda suka ɗauke ta bawai kasheta akai ba,zuwanka shine zai ƙara tabbatar maka" shuru yayi na wani lokaci kafin yace "ok yallaɓai C.P ina gdy sosai saika zo ɗin" yana faɗin hakan ya shige cikin gidansa ba tare daya kalli Deen dake zaune ba..
Misalin ƙarfe 11 na dare gidan yayi shuru ba kajin kukan komai saina gyare dake ta faman kuka "tsut tsut tsut" wata babbar akwati Deen ya buɗe ya kallin Moon dake bacci ta rungome teddynta hannunta riƙe da chocolate wani shu'umin murmushi yyi kafin a hankali ya ɗauke ta cak ya ya sakata cikin akwatin da sauri ta buɗe idanunsa sbd zafin da taji,kallonsa tayi shima ya kalleta tana ƙoƙarin kiran sunansa yayi saurin dannata cikin akwatin tare da zuge zip ɗin...

😱😱😱tab ɗin team Moon how far..?

_afuwan da jina shuru da kukai na shiga busy na biki amma Allhamdulillah mun kammala cikin farin ciki da kwanciyar hankali🥰abu na biyu na faɗa muku duk bayan ƙwana biyu zanna posting sbd ina book ɗin Uncle ne kuma na kuɗi ne nake ending na book 1 duk mai buƙatar siya sai yyimin mgn 08119237616_

*Tabbas idan ba'a comments da share zan ajjiye book ɗin,ko kuma ya koma na kuɗi tunda kunfi gane haka😂😂*


SARAUTA👑

MOONWhere stories live. Discover now