4

96 8 0
                                    

ASHRAF: Beauty meets Ugly

04




Duk abinda aka ce ƙaddaranka ne to fa ba zai taɓa wuce ka ba.
Da Asuba da Qayyisah ta tashi ta buɗe datar wayarta sai ga shigowar email.

Dan kada ma hankalinta ya tashi tun bata yi sallah ba ta ajiye wayar ta shiga banɗaki, amma kam zuciyarta cike da taraddadin ina aka turata.

Ta idar da sallah tayi azkar tareda addu'ar Allah yasa koma ina ne dai Allah yasa Baba ya amince da wajen.

Ta ja dogon numfashi sannan ta ɗauki wayarta da Bismillah. Tana buɗe gmail ɗinta ta fara bin layi da layi tana karanta call-up letter ɗin da aka turo.

Ta shiga ƙyafƴyafta ido dan bata yarda da abinda take gani ba.

Ta kifa wayar akan gado tana tunanin anya ba idonta  ne ke ganin abinda zuciyarta ke son gani ba.

Chan ta ɗau wayar ta kira numbar Zaidu. Gara shima ya zo ya gani dan ta tabbatar da ko dai gaskiya Abujan aka turata ko kuma idonta ke mata gizau.

"Chaɓ! Kice bakin Anty Fa'iza ya kama ki" Zaidu ya faɗa lokacin da ya karanta call-up letter ɗin.

"Zaidu da gaske Abuja ne ?"

"Kin ɗauka wasa ne. Ai ki haɗa kayanki kawai za ki Asorock"

Qayyisah ta maki kafaɗarsa " it's not funny Zaidu. Ka san Baba ba zai amince ba"

"To ina ruwan NYSC da abinda Baba yake so. Inba Baba bama ai ba lallai ma cikin Abujan za a posting ɗinki ba"

"Idan ma cikin Abujan ne ai ba abinda zai haɗa ki da gidan Abba"

Qayyisah ta yi Hmmm.

Ita ba wai dan zuwa gidansu Abba yasa take son zuwa Abuja ba. Saboda Nura ne.
Ta sani babu abinda ganin Nura zai yi mata. Amma deep down tana son sanin ko Nura ya taɓa tunawa da ita. Ko yayi dana sanin abinda yai.
Daɗin daɗawa tana son yi masa tambayoyin da bata samu daman yinsu ba a wancan lokacin.

Tana son sanin ko ya taɓa sonta ko kuma dama tun asali yaudararta yai.

A lokacin uzurin daya faɗa yasa ta manta da maganar yaudara.

A lokacin gani take tunda akan aƙidar Baba ne gara ta haƙura da shi dan kar hankalin Baba ya tashi.

Lokacin da suke soyayya ba abinda bai sani akanta ko akan Baba ba.

Hatta yadda mahaifiyarta ta rasu sai da ta gaya masa.
Ta gaya masa abinda bayan iyayenta babu wanda ya sani babu wanda ta taɓa faɗawa wannan labarin.

Ta gaya masa cewa ita ce sanadin ɓatan Humairah ko kuma tace kisan Humairah.
Duk da dai Baba yace gawan data gani bana Humairah bane. Amma har yanzu tana ji a ranta cewa baƙin gawan data gani na Humairah ne.

Shima Nuran ce mata yai ba gawar Humairah bane. Wai ta ɗauka cewa Humairah ko ɓata tayi ko mutuwa ta yi ba laifinta bane, haka Allah ya tsara.
Mutane dayawa sun rasa danginsu a rikicin Jos.
Dama ai koma bayan kowanni faɗa ko yaƙi tashin hankali ne da kuma asaran rayuka da dukiyoyi.

Nura ya san komai nata. Ya san komai daya kamata ya sani kafin ya turo iyayensa.
Wai ma idan ba munafurci ba mutanensa basu yi bincike bane kafin su zo. 
Wai sai da aure ya zo gab. Sai da aka printing invitation cards, aka yi kusan kaso 80% na aure zasu fito su soki aƙidar mahaifinta.

Abin haushinma Nura bai iya gaya mata baki da baki ba sai turo mata mummunan text yayi.

*I'm sorry My Zee* tsabar ƙarfin hali sai da ya haɗa da MY ZEE dan ya ƙunsa mata baƙin cikin da kyau.

ASHRAF -Beauty meets Ugly (Hausa Romance Novel)Where stories live. Discover now