Kallon ta El'mustapha yayi, kafinYace uwar amarya an dawo kenan.
Ta qarasa cikin dakin, shimfidar da airah tayi tana kallonsa,
Me ya hana ka barci tuntuni el'mustapha?
Rashin barci nawa kuma ya xama abin tuhuma yanxu jiddah, lallai
Sai ya gyara kwanciyarsa hade da lumshe idanunsa,
Ta tabe baki ta xauna tana fadi a ranta in ma banan ce ta riga ta xamo matar wani a yanxu.
Pampers ta soma sakawa airah, tayi feeding din ta kafin ta kai ta saman bed din ta, ta kwantar da ita, ta rage hasken fitilar dakin ta dawo bayan el'mustapha ta kwanta.
Haka take ji cikin kashi 70 na damuwar ta 30 ya kau, uwani ce babbar matsalarta a yanxu kuma bata san yanda xata bullowa al'amarin na ta ba.
Ta sauke numfashi a hankali tana kallon el'mustapha tuni ya jima da yin barcinsa, ta lumshe idanuwanta tana karanto addu'ar barci a xuciyarta.
*
Kuka take tana qarawa, lallai sai an maidata dakin ta.
Saboda baa sona ba wanda ke maganar yayi min aure a maidani dakin mijina abin sona, banan ma da take mai aiki anyi mata aure, ta auri miji mai kyau da kudi sai dan ni da ake ma baqin ciki anqi a maidani dakin mijina.
Sam hajiya bata kula ta ba, ta cigaba da hada kayanta saboda gobe xasu bar garin
Uwani ta tashi ta fito daga dakin taci sa'a kuwa el'mustapha ya fito xai je aiki,
Ta sunkuya tana fadin yaya an tashi lfy, yaya kayi haquri ka yafe min kuskuren da nayi a baya dan Allah ba danni ba ka yafe min, ka roqa min anti jiddah ta yafe min mu dawo tamkar da, dan Allah yaya ka taimakeni nima qanwar kace kuskuren da nayi a baya jarabawa ce da qaddara da bata wuce bawa.
Shikenan ki tashi komai ya wuce... yana maganar ne fuskarsa a daure,
Yaya a bani key din daki na xanje na gyara, yaushe xan fara karban girki.
Kafin yayi magana sai ga jiddah ta fito duk da bata ji me uwanin ke fada ba amma tayi mamakin samun uwani da el'mustapha a falon ta, gabanta ya tsananta bugawa.
Idan hauka ke damun ki uwani, na fiki hauka a yanxu indai akan el'mustapha ne, wallahi in baki barshi ba xan iya halaka ki ban damu ba.
Uwani ta tashi tana fadin haquri naxo na baki anty jiddah ki yafemin kuskuren da nayi a baya wallahi sharrin qawa ne, ni yanxu xuciyata a wanke take da alkhairi baxan cutar dake ba, ki qara roqon yaya ya aure ni ko baya da kudin sadaki ni xan iya ara masa, idan key din dakina yana hannunki ki bani naje na gyara.
Jiddah tace tau shikenan bari na baki, ta juya da sauri kamar mai neman wani abu
Ta rasa me xata dauka, kujerar dinning ta dauka tayi kan uwani a fusacce,
Uwani na ganin haka tayi bayan el'mustapha da gudu tana fadin,
Aa yaushe anti jiddah ta fara hauka kuma shine abba bai kaita itama a duba ta ayi mata aiki ba,
El'mustapha ya tare jiddah da sauri,
Me kike yi haka jiddah, kashe ta xakiyi?
Ko sauraren sa batayi ba tayi bayansa suka soma xagayen sa yana tsaye a tsakiyarsu, ya kalli wannan ya kalli waccan,
Lallai basu da hankali, wani abu ya taba kan jiddah indai ba gurin aikin bane aka taba kwakwalwarta,
Ya tsaida uwani cikin bacin rai yana kallon jiddah,

YOU ARE READING
El'mustapha
Romance'Mijin yar'uwata nake so, farin cikin da yake baiwa matarsa nake son samu fiye da hakan, so nake na rabashi da matar sa da ya'yan sa ya zamto ba kowa a xuciyar sa sai ni. El'mustapha ya shiga cikin rukunni wasu mutane da nake ganin matuqar qima da...