*DESTINY LOVE*
Daga alƙalamin
*Oumyasmeen*
Watt pad @Aminaoumyasmeen
Arewabooke@oumyasmeen
Perfectly pen's ✊
KING AND QUEEN WRITING CHAMBER👌✊
Episode 56-57
ƙasa yayi da kansa yace
"Mata tace basu labarin abin da ya faru yayi
Tuni gun suka ɗauki salati ban da safna da ta zube basu sani ba kuka sitti tasa ta fyace majina tace
"Ubaidullah kaji abin da ɗanka kake faɗi ko baka fasa mai baki ba saboda ya raina ni na zaɓa mai mata shine yaje ya kwaso mana farar fata baya hudiya wallahi bazata zauna min a gida ba...,
ɗago da runannun idanuwansa yayi ya kafe sitti da su jin kalamanta na karshe a hankali ya buɗe baki yace
"Sitti kin manta baya....? me ya faru
Hmmm ya saki wani muskilin murmushi yace
"Gurin da nake zaune da kuɗina na siya da gumina na gina da kofar shi ba a cikin gidan nan take ba sai da uncle yayi min magana na tushe kofar na shigo da ita yanzu ma ina da yancin mai da ita inda take zama da ita ba gudu ba jada baya....,
Salati sitti ta saki tace
"Kana ji ɗanka yana gasan magana kayi shiru.... Ko to wallahi dani kuke zance kuma yau ɗin nan safna zata tare a gidansa,
dafe kai salim yayi yaushe tareek ya auri safna be sani ba itama bata faɗamai ba lallai akwai kura yanzu ainiyin wasan zai fara wato ko ta wanne fanni tareek ya fishi shida ma yake shege tab jajar ubannan.....
alhaji Ubaidullah ya gyara zamansa yace
"Muhammad kar in ƙara jin bakin ka sannan yau ka tattara kayan ka guri ɗaya safna zata tare,
Ɗago hajayen idanuwansa yayi ya dubi mahaifinsa sai a kai sa'a suka haɗa ido da uncle nasir girgiza mai kai yayi ya na yimai alama yabi umarnin mahaifinsa cije lips ɗin sa na ƙasa yayi motsa lips ɗin sa yayi yace
"To,
Alhaji Abdulnur da Alhaji Abdullah ransu be soba da sitti ba takori tareek ba musanman alhaji Abdullahi da suke yar tsama yana da gidan yin robobi to chemical ɗin yana cutar da al'umma sai aka kai shi ƙara gidan Radio
shine ya jagoranci shirin har cin hanci ya bashi akan ya danne abin amma yaƙi haka shugaban gidan Radio ya bashi umarni kar ya yaɗa shirin yaƙi ya yaɗa dan haka ya salame shi shine yanzu Alkhairi radio ta ɗauke shi aiki
gyara zama yayi yace
"Allah ya ja da ranki sitti amma wannan yarinyar mece makomar ta a gidan nan gaskiya bazai yuhu ba kin haɗa ƴa'ta da tareek amma banyi magana ba duk da irin tawayar da yake da ita be gani ba ya kara ɗauko wata gaskiya baza ta saɓo ba ...,
wani irin numfashi tareek ya fesar me huci fuskarsa tayi ja riƙe hannun gujerar sitti yayi gam har hannunsa na jini saboda ruƙo da yayi
kurawa kahunsa ido yayi ko kiftawa bayayi besan lokacin da ya ture Centre table ɗin dake gan bansa ba
jikake tararatsar ga bada sautin tush a binka da glass da sauri mom hafsa da mom amina suka takure gu ɗaya sun san halin haukan tareek zai iya daukan mutum yayi hulli dàshi miƙewa yayi ya riƙe hannun abrar ya fara tafiya

KAMU SEDANG MEMBACA
DESTINY LOVE
Romansadabi'ar family ne ba ruwan wani da wani tamkar bajini daya ba wata iriyar kaddararriyar rayuwa suke me ban mamaki da tsoro haka ya samo asali daga iyayen su sun nuna son ya'yansu dan uwanka be isa ya tsawatar wa da ya'yan dan uwansa ba ran kakansu a...