MAMAYA Last page

487 45 4
                                    

*👺🤡MAMAYA👺🤡*

*NA*

*HAUWAU SALISU*

*MAGA_TAKARDAN KAINUWA CE ✍🏻*


*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

07081095452

My Gmail👉🏻
*Hauwausalisu407@gmail.com*

My Facebook 👉🏻
*Hauwa'u Salisu(Haupha)*

My Wattpad 👉🏻 *Hauwausalisu*
https://my.w.tt/P1yNEVRFl3

My You tube channel 👉🏻https://youtu.be/h6gc8ahxrmM

Last page 61--70 ✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻✍🏻

Aljana Raƙiyyatul Zayyanul murrash, tana sauka dajinsu ta yanke jiki ta faɗi cikin galabaita.

Sarki Zayyanul murrash yana zaune yana ganin dukkan abubuwan dake faruwa, cikin sauri ya ɓace ya bayyana gaban Aljana Raƙiyyatul Zayyanul murrash ya yarfa mata wani ganye dake ɗauke da ruwan magani take a suka ɓace daga gun.

Can ɗakin tsafinsa suka bayyana, kan wani tsohon gadon kara ya kwantar da Aljana Raƙiyyatul Zayyanul murrash, ya ɗauko wasu kayan tarkacen magani ya fara surutui yana yarfawa a jikinta.
Nan da nan ɗakin ya turniƙe da hayaƙin gaske ko tafin hannu ba a gani tsabar duhu.

Ya jima yana mata abubuwa sannan sai ga wani haske ya bayyana ya shige jikinta, sai gata wuf ta tashi zaune tana kallon mahaifin nata.

"Ya kai Abbana bani labarin abubuwan da suka faru . Shin ya Nasir ya kasance da masoyiyarshi ?

Dariya mai amsa kuwa ya kwashe da ita, sannan ya turniƙe fuska yace,
"Ki kwantar da hankalinki domin komi ya wakana yadda kike so, yanzu haka Nasir da Bilkisu suna tare cikin iyayensu."

Duban mamaki take ma shi ta ce, "Shin me ya samu Nasir da Bilkisu ne ? Ni da muka je amso Inna Huraira me ya sako Nasir da Bilkisu ciki?

A hankali ya bata labarin duk abubuwan da suka faru, bayan komawarta gunki .

Sosai abin yayi mata daɗi, don haka ta miƙe ta shige wani ɗaki dake kallon ɗakin da suke ciki.

Ko da shigarta ta kira hadimanta data tura gidansu Bilkisun don su zauna matsayin Bilkisu da Huraira.

Cikin ƙanƙanin lokaci suka bayyana suka labarta mata yaƙin da sukai da hadiman Abduljalal bin Uwais.

Cikin sauri ta ce maza ku koma ki bibiyomin labarin abin da ke faruwa yanzu, domin raina na bani akwai abin da ke faruwa ga Nasir."

Cikin lokaci suka ɓace suna mai rusunawa gareta.



         Abduljalal

Tunda suka tafi da Bilkisu yake kuka kwance kan cinyar Suwaibatul Zabbar ya fita daga hayyacinshi duk tausayinshi ya kamata, kuka yake kuka take har ta fara jin cewar ya kamata ta ɗauko Bilkisun ko don kwanciyar hankalinshi .

Cikin kuka ta dube shi ta ce, "Jalal ko dai na je na dawo maka da farin cikinka Bilkisu ?
Ka sani ni ba zan lamunci zamanka cikin wannan mugun hali ba.
Ka sani kai ne farin cikina, ba zan iya barinka a wannan yanayi ba sam.
Nasan cewa kai kuma ita ce farin cikinka don haka zan dawo maka da ita don rayuwarka ta tabbata cikin farin ciki."

You've reached the end of published parts.

⏰ Last updated: Dec 27, 2020 ⏰

Add this story to your Library to get notified about new parts!

MAMAYAWhere stories live. Discover now