MAMAYA Page 46-47

529 50 3
                                    

*👺🤡MAMAYA👺🤡*

*NA*

*HAUWAU SALISU*

*MAGA_TAKARDAN KAINUWA CE ✍🏻*


*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

07081095452

My Gmail👉🏻
*Hauwausalisu407@gmail.com*

My Facebook 👉🏻
*Hauwa'u Salisu(Haupha)*

My Wattpad 👉🏻 *Hauwausalisu*
https://my.w.tt/P1yNEVRFl3

My You tube channel 👉🏻https://youtu.be/h6gc8ahxrmM

Page 46---47

Luf tayi tana jin wani yanayi mai kama da sarewa ko sallamawa, sai dai taci burin duk daren daɗewa sai ta ɗauki fansar wahal da ita da mahaifiyarta da yayi.

Abduljalal bin Uwais ya ɗago kanta yana ƙare mata kallo.

Wani masifar sonta na yawo a cikin gaɓɓan jikinsa, cike da shauƙi ya ɗago fuskarta .

"Bilkisu kin MAMAYE NI da kika saka na afka sonki bayan ni da zummar ɗaukar fansa na zo gareki, amma kika ringayeni da kyawawan halayenki kika sa na wayi gari cikin ƙaunarki."

Ita dai batace ƙala ba, jin yanda tsanarsa ke yawo cikin jikinta baki ɗaya.

Sai da ta samu da ƙyal ta haɗiye baƙin cikin dake cike da bakinta tace.

"Yah Malam mi ne ne ya saka Inna cikin lamarin ɗaukar fansarka ?

Shin itama ta jefeka ne ?"

Murmushi yayi mai sauti ya shafi fuskarta yace,

"Ita kam laifinta guda ne, bata da ilimi tana fama da jahilci mai girman gaske, dan haka suke wasa da ita saboda tana sasu nishaɗi ko da yaushe.

Amma a yau zan sa a maida ta gida cikin ikon Allah, sannan nasata makaranta tayi ilimi yanda ya kamata a yanzu Huraira tasan daɗin addini yanda ya kamata, bata da matsala yanzu akan addini Huraira.

Ya ja hannunta sai gasu sun bayyana cikin wani ɗaki mai kyan gaske, Inna Huraira zaune tana duba Kur'ani sai da Bilkisu tayi mamaki jin yanda da gaske Inna ce ke karatu cikin natsuwa da ƙwarewa.

Ta jima tana kallon Innar ba tare da ita Innar tasu ta ganta ba.

Komawa su kai wata kyakkyawar fada duk kuyangi da bayi sunata hidima.

Kan kujerar data sha kayan ado ya kaita ya zaunar da ita .

Cike da girmamawa fadawan suka dinga kawo gaisuwa gareta ana mata kirari .
Duk abin nan zuciyar Bilkisu kamar zata fashe dan baƙin ciki da takaici, wai ita ce ta auri aljani? Allah ya saka mata ya fidda mata haƙƙinta jikinsa.




Yana zaune gaban kayan tsafinsa, ya kwarara ihu, ya fara zunduma ashar kala daban-daban, baki ɗaya ya fice daga hayyacinsa saboda tsabar ɓacin rai.

Sarki kuma boka Zayyanul murrash bin zainul kenan, lokacin daya ga abin da ya faru ga tilon ɗiyarsa Aljana Raƙiyyatul Zayyanul murrash a cikin dajin Abduljalal bin Uwais.

Haƙiƙa da yasan da tafiyar Raƙiyyatul da bai barta ta kusa kai cikin dajin ba, domin duk wanda ya shiga dajin indai ba musulmi bane sandarewa yake a tsakiyar dajin.

MAMAYAWhere stories live. Discover now