MAMAYA page 33---35

559 50 9
                                    

Karku manta kuje You tube channel ɗina mai Suna HAUPHA TV kuyi mun SUBSCRIBE tare da danna kararrawa 🔔 domin samun littafaina cikin Audio .

Hauwa'u Salisu (Haupha)✍️

*👺🤡MAMAYA👺🤡*

*NA*

*HAUWAU SALISU*

*MAGA_TAKARDAN KAINUWA CE ✍🏻*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

07081095452

My Gmail👉🏻
*Hauwausalisu407@gmail.com*

My Facebook 👉🏻
*Hauwa'u Salisu(Haupha)*

My Wattpad 👉🏻 *Hauwausalisu*
https://my.w.tt/P1yNEVRFl3

My You tube channel 👉🏻https://youtu.be/h6gc8ahxrmM

Allahumma ajirni fi masibati wa akhlifni khairan minha ya Allah.

_Alhamdulillah! Komi ya samu Bawa da sanin Ubangijinsa, ina godema Allah aduk halin da nasamu kaina ._

Page 33----35

Shema'u na zaune ta zubama Bilkisu ido sai kallonta take, ba ƙaramin mamakin halin da ya sakata cikin wannan yanayi take ba, duk da tasan kaɗan daga matsalar Inna Huraira batai tsammanin matsalaice ta sakata cikin wannan halin,amma  dai bari ta jirata ta tashi taji gaskiyar lamarin daga bakinta. Ganin tana zaune haka ba wani abu sai tunanin zuci yasa ta jawo wani littafi dake gefen Bilkisun ta soma karantawa,sai tun a shafi na farko ta ɗago ta kalli Bilkisun domin ganin abin da ke cikin littafin, murmushi tayi taci gaba da karantawa tana mamakin yaushe Bilkisu ta ƙware da iya tsara kalamai haka ? Bama kamar gunda taga ta saka cewa "Ka taimaka ka dawo gareni ko kafafuwana kunnuwa tare da zuciyata su sami salamar rayuwa cikin aminci, Ibnah rashinka kusa dani ya jefani makarantar gararanba wadda kullum sai zuciyata ta wahala gangar jiki tayi nauyi." Sosai Shema'u ke dariya ashe Bilkisu munafukace ta iya soyayya irin wannan baka ganewa ko a fuskarta ? Cikin sauri taci gaba da karanta littafin wanda baki ɗaya duk kalamai ne masu ratsa zuciya ke rubuce cikinsa,ganin bata gama karantawa ba ga Bilkisun na niyyar farkawa daga barcin ta ɗauke littafin ta fice dashi daga cikin gidan.

Yana dawowa da madara a hannunsa da wani magani ya kwaɓa cikin ɗan kofi ya nufi gun magen, tana a yanda ya barta kuwa amma barci take ga alama na wahala ne, dan haka ya tadata ya kafa mata kofin saitin fuskarta, ai kuwa ta kama sha ba ƙaƙƙautawa sai da ta kusan shanye madarar kana ta janye kanta taci gaba da lashe bakinta. Sosai yake kallonta yana mamakin kansa domin shi bai wani damu da sabgar maguna ba balle har ya tsaya tarairayarta, asalima yasha korar ta wani soja dake zuwa ɗakinsa lokacin yana Nasarawa zaune amma yau shine da nemo mata abinci dasu magani ! Lallai  abin da mamaki .

Wayarsa ya janyo ya kira number ta Amma harta katse bata ɗaga ba, murmushi yayi mai sauti yasan tana can tana barcinta har yanzu kenan, a fili yace "Ibnah ba dama."

Malam Aminu komi ya kwance masa kai tsaye yake jin soyayyar Bilkisu na tasowa ta ƙasan zuciyarsa tana game dukkan ilahirin jikinsa, komi yake fuskarta yake gani, komi ya tsaya masa cak, yana jin ita kaɗaice wadda ta dace dashi a wannan rayuwar, domin komi nata yayi masa, sai dai bai san yanda zai yi ya gaya mata yana ƙaunarta ba, zuciyarshi ta bashi shawaran kai tsaye yaje ya faɗa mata yana sonta! Wata kuma tace ka dai je gun ƙawarta Shema'u ka aiketa da saƙonka sai yafi maka sauƙi, haka yayita saƙawa yana kwancewa har ya aminta da zai tari Shema'u da maganar domin ta shige masa gaba kan lamarin soyayyarsa da ƙawarta Bilkisu.

MAMAYAحيث تعيش القصص. اكتشف الآن