MAMAYA page 27_28

444 53 0
                                    

*👺🤡MAMAYA👺🤡*

*NA*

*HAUWAU SALISU*

*MAGA_TAKARDAN KAINUWA CE ✍🏻*


*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

07081095452

My Gmail👉🏻
*Hauwausalisu407@gmail.com*

My Facebook 👉🏻
*Hauwa'u Salisu(Haupha)*

My Wattpad 👉🏻 *Hauwausalisu*
https://my.w.tt/P1yNEVRFl3

My You tube channel 👉🏻https://youtu.be/h6gc8ahxrmM



Ina godiya gareku masoyana tabbas kuna mun abin da ya kamata dan haka nima nake ta ƙoƙari dan ganin nayi maku abin da ya kamatan, pls kuyi mun subscribe channel ɗina Haupha Tv domin cigaba da samun littafaina ta can kai tsaye .


Page 26____27

Cikin sauri suka nufi  ɗakin Huraira banda addu'ar Allah yasa burinsa ya cika babu abin da Malam Ummaru ke yi, yayin da shima a nashi ɓangaren malam Shehu mai Tawada fatansa marar lafiyar ta kasance irin tasa yanda zai ce akai masa ita gidansa yayi mata maganin acan.

Gaba ɗaya Huraira ta shiga cikin mayuwacin halin yin arbarta da wata mummunar halitta wadda tunda take gane-ganenta bata taɓa ganin irin wannan mummunar halittar ba, buɗe baki tayi da nufin kwartsa ihu sai ga wani ƙaton hannu yayi fitar burgu daga cikin bakin halittar ya nufi Huraira ya daɗe mata baki gum.

Wata narkekiyar halittace mai manyan kunnuwa sama da goma kanta guda ɗaya ne amma ya cika ɗakin ga wani irin idanuwa masu kama da idanun damisar dawa irin wadda ke jin yunwa taga nama, jikin kumatunta kuwa sun tsattsage wasu tabka-tabkan manyan tsutsoci na fitowa suna shigewa cikin bakinta tana taunewa, gaba ɗaya jikinta wani irin gashine marar kyan gani ta zazzalo harshenta waje wasu allurai sun fito saman halshen kamar an dasasu, haƙoranta wasu irin jajaye gasu da mugun tsini tamkar bakin mashi, madadin gashi ita kanta wasu tabka-tabkan manyan macizaine saman kan ƙaton kan nata sai motsi suke suna buɗe bakunansu, ga wasu  manyan hannuwa sun kai bakwai kowane da akafar da tayi tsayi na ban mamaki, cikin wata ƙatuwar murya ta dakama Huraira tsawa "Ubanwa yace ki ɓatamun aiki ? Sautin muryaita yasa Huraira sulalewa a sume gun ita kuma ta zama hayaƙi ta shine cikin jikin Huraira.
Nan take Huraira ta bingire a gun ta cigaba da sheƙa barci mai nauyi.

Malam mai Tawada shine kan gaba gun shiga ɗakin, musamman da ya ji tsit ko irin ɗan kururuwar nan bata yi sai yaji a ransa yau ko shakka zai samu ta sauyawa yau dan haka ya juyo ya kallesu yace "Ku dakata daga nan ni zan dubata kun san irin waɗan can shauɗanun basu san yawan mutane a gunsu dan Allah ku yi zamanku a can (ya nuna kofar ɗakinsu Bilkisu) kuyi ta addu'a kuna ƙarawa ni zan shiga nayi masu aikin gaggawa" ya shige cikin ɗakin hada su gyara labule, malam Umaru yayi kamar zai bishi cikin ɗakin, ai da sauri mai Tawada yace "A'a Malam koma can kaima dan aikin bana wasa bane ba. Shi kam malam Umaru banda dariya ƙasan ransa ba abin da yake, musamman da yaga sai wani zumuɗi yake dan haka yace "Wai da tare maka hanyar zan kada ta rugo kasan Aljanu da tsoron irinku ai " hakan yasa mai Tawada yace "Anyi haka fa, to ka ja mana ƙofar kada su ruga a rasa mai kamosu kam.
Cikin matuƙar farin ciki malam Umaru ya ja ƙofar ya rufe gam dasu rataya ɗan makullin dake jikin ƙofar, hakan yasa Bilkisu yin magana cikin alamar rashin yadda da abin da ke faruwa na rufe Inna tare da wani cikin ɗaki su kaɗai, malam Umaru ya dubeta ya ɓata rai sosai yace "Dan gidanku Bilkisu ke zaki gayama abin da ya kamata muyi ne ? To bari kiji gaskiyar magana ana fara mata ruƙiyya ta ɓalle ta ruga duk cikin anguwar nan ba mai iya kamota. Jin hakan yasa tai tsit ta shige ɗakinsu tana share hawaye kawai, Malam Umaru ya dubi bayanta yace "Kaga ja'irai yarinya na neman ta rusa mun duk wani bajat? Ya ciji leɓe ya sake gyara kwaɗon ya koma gun yaran Malam Shehu mai Tawada ya zauna yana addu'ar Allah yasa yau mai Tawada ya gane kurensa.

MAMAYADonde viven las historias. Descúbrelo ahora