MAMAYA PAGE 51---55

518 47 15
                                    

*👺🤡MAMAYA👺🤡*

*NA*

*HAUWAU SALISU*

*MAGA_TAKARDAN KAINUWA CE ✍🏻*


*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

07081095452

My Gmail👉🏻
*Hauwausalisu407@gmail.com*

My Facebook 👉🏻
*Hauwa'u Salisu(Haupha)*

My Wattpad 👉🏻 *Hauwausalisu*
https://my.w.tt/P1yNEVRFl3

My You tube channel 👉🏻https://youtu.be/h6gc8ahxrmM

Page 51----55

Zayyanul murrash ya dubeta fuska ba alamar wasa yace, "Idan kin aminta za ki ƙwato min yarinya ta sarauniya Raƙiyyatul Zayyanul murrash, sannan sharaɗi na biyu za ki kashe masoyiyar Abduljalal bin Uwais , to haƙiƙa ni nan zan taimaka maki da yadda za ki kashe yarinyar cikin ruwan sanyi."

Dariya ta bushe da ita, kamar an tarwatsa dutse, kana ta murtuke fuska ta dubesa ta ce, "Na sanka baka da amana baka san darajar alƙawari ba Sarki Zayyanul murrash, domin kuwa ku cin amana a cikin ibadarku take, ha'inci a cikin jininku yake, yaudara ita ce takenku.

Amma duk da haka bari ka ji wata magana, zan amince da wannan sharaɗi naka idan kaima ka amince da nawa sharaɗin.

Ka sani idan na kashe Bilkisu na kawo maka Raƙiyyatul Zayyanul murrash ka ce zaka ci amanata ta hanyar cutar da Jalal ɗina na rantse da Sarkin da ke busa ma matacce numfashi da kai da ita tare da duk magoya bayanka sai na halaka ku na ɓatar da ku daga doron duniyar baki ɗaya.

Kasan cewar nafi kowa baƙin hali, baƙar zuciya da taurin kai harma dana rai a cikin jinsinmu .

Dan haka ka tabbatar da cewa baka da burin ɗaukar fansa akan abin da Jalal yayi ma ƴarka Raƙiyyatul Zayyanul murrash .

Sannan ina son ka sani sai na shafe babin duk wasu masu bautar gunki da tsafi a wannan duniyar, kasan zai zan iya ko ?

Wata banzar dariya ya kwashe da ita mai ban takaici ga wanda akai mawa ya nuna wani madubin tsafi dake kafe a cikin ɗakin.

Sai ga hoton Bilkisu da Abduljalal bin Uwais, Bilkisu na kwance jikinsa yana shafa cikinta yana murmushi ya kai bakinsa ya sumbace ta a cikin yace, "Ya ke hasken idaniyata muradin zuciyata farin cikin raina, shin yaushe za ki sanyaya idaniyata da kyakkyawar ɗiya ko ɗa ne ?

Shafa fuskarsa tayi tana mai maida masa martanin sumbata a fuskarsa ta ce, "Ina roƙon Allah ya ban yaro kyakkyawan gaske kuma jarumi haziƙi kamarka masoyina."

Bakinta ya rufe yana murmushi yace, "A son raina na fi son ace kin haifi yarinya kamarki sak, da irin halayenki na tabbata da na fi kowane uba samun farin ciki a duniyar nan."

Wata uwar ƙara Suwaibatul Zabbar ta saka ta dinga marin fuskarta tana yakushin idanunta da suka gane mata wannan babban lamari .

Sarki Zayyanul murrash ya ɓarke da dariya yace, "Na rantse da abin bauta ta idan kika kashe yarinyar nan kin gama da duk wata damuwa taki, sannan idan kika maido min ɗiyata zan baki mamaki ta hanyar zama hadiminki .
Kin san dai na kasance ɗaya daga cikin masu cika alƙawari, sannan ban wasa da rayuwar ɗiyata ɗaya tal da na mallaka a rayuwata bayan shan gwagwarmayar rayuwa.

MAMAYAWhere stories live. Discover now