MAMAYA page 29--30

459 48 3
                                    

*👺🤡MAMAYA👺🤡*

*NA*

*HAUWAU SALISU*

*MAGA_TAKARDAN KAINUWA CE ✍🏻*

*بسم الله الرحمن الرحيم*

*____________________________________*

*🌈KAINUWA WRITERS✍🏼 ASSOCIATION*🤝🏻
'''{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation

*____________________________________*

07081095452

My Gmail👉🏻
*Hauwausalisu407@gmail.com*

My Facebook 👉🏻
*Hauwa'u Salisu(Haupha)*

My Wattpad 👉🏻 *Hauwausalisu*
https://my.w.tt/P1yNEVRFl3

My You tube channel 👉🏻https://youtu.be/h6gc8ahxrmM


Page 28____30

Nasir na kwance yana tunanin halin da yabar masoyiyarsa, jiyake kamar ya aje aikin dan yanzu ya fara takura masa gun kusantar Ibnarsa duk sanda yaso ko yaga dama, misali ranar da suka rabu asibiti ya dawo gida ya hana ƙannensa zuwa gidansu yana da burin washe gari ya kwashesu suje baki ɗaya sai ga wayar gaggawa daga office ɗin su ana nemansu da gaggawa,dole ya shirya ba dan yaso ba ya wuce, abin takaicinsa guda ya kira number Ibnar tasa a kashe kada ace dai ciwon dawowa yayi ? Gaba ɗaya ya rasa kuzari da walwala duk a takure yake dan haka yaransa ke baya-baya dashi musamman da suka fahimci yana tare da damuwa,sai kowa ya kama kansa, dan Nasir ba baya gun zuciya da fusata bai cika wasa ba.

"Tunda na haɗu da yarinyar nan komi ya lalace mun, na rasa da dama daga kimata da darajata ni kam nayi alƙawarin shirya mummunan sakayya gareta domin samun sauƙin yanayin data jefa rayuwata cikinta. Gaba ɗaya sun sadda kansu ƙasa suna saurarensa a ƙalla yau anyi wata biyar Sarkin nasu ya kasa aiwatar da abin da yake cewa zai aiwatar, tabbas yanzu bai da tarin iko mai tafe da karfin izza tunda har wata jaririya daga cikin yaran bil'adama tasha gabansa take wahal dashi tafi karfinsa tafi ƙarfin yaran fadar tasa, lallai suna da buƙatar sauya Sarki kada wata rana suna sake da baki ya jawo masifar da zatasa aci su da yaƙi a banza. (Gaba ɗaya abin da yan majalisar fadar ke rayawa a cikin zukatansu kenan akan Yah Malam).Ganin sun shigo cikin ɗakinsa sun yi zugum-zugum sai ransa ya sake ɓaci, zuciyarsa ta hasala nan take ya fara narkewa yana zama wani baƙin ruwa mai kama da tafasasshiyar dalma yana tururi da hayaƙi, ya nufosu , ai take suka fara zaro idanuwa waje domin sun san cewa duk wanda wannan ruwan ya taɓa shikenan shi angama da babinsa, domin toyasu yake ba tuyar arziki ba,cikin tashin hankali suka fara bashi haƙuri suna ja da baya,amma sai da ya mamaye wajen Aljanu hamsin sannan yayi tsiri sama ya zama gajimare ya ɓace bat.

Tunani take hawaye na zuba ta gefen idonta, tabbas akwai yiyuwar Innar tasu ta datse mata soyayya da wanda yanzu ne ta fara fahimtar yanda ƙaunarsa tabi jini da tsoka na jikinta, ta sake jawo wayar ta dubeta ko zata ga kiransa ko message nasa amma ba ko ɗaya da tagani, cikin kuka mai ɗaci tace "Ibnah karkai mun haka dan Allah, domin kaine mabuɗin jin daɗin lamarina tare da sanyaya rayuwata, haɗuwata da kai yasa na fara samun natsuwa da kwanciyar hankali, karda kasa na fara tunanin na zamanto ɗaya daga cikin waɗanda basuyi dace a soyayya ba,karka manta kaine wanda ko da yaushe kake jadadda mani yanda kake ƙaunata tare da son farin cikina, Ibnah idan har kace ka haƙura dani saboda Innata tabbas ka shiga rayuwata" kuka ya ƙwace mata mai karfi wanda sai da ƙannenta suka zagayeta suna tambayarta "mi take ma kuka? Cikin rashin tabbas dana sanin abin da zata furta masu ta share tambayarsu ta rungume su tana sake jin wani kukan mai karfi ya sake kucce mata, suma kukan kawai suka saka abin da ya jawo hankalin Inna Huraira kenan ta faɗo ɗakin har tana tuntuɓe " Na shiga ukuna ni Huraira kukan mi kuke ku kuma? To wallahi sai dai ubanku ya mace ba dai Huraira ba, ƙaryar banza ƙaryar wofi, duk nasan nufinku ai bama kamar yayar taku to wallahi sai Malam ya rigani mutuwa ƴan banza, kuna rufe mun baki ko sai jikinku ya gaya maku ne ? Ta rarumo kofi dake aje ta matso gabansu, tsit su kayi ba wanda ya sake ko tari, musamman Bilkisu da tasan ba ƙaramin aikin Innar tasu bane ta zane ta tsab ba. Cike da masifa tace maza ki tashi ki shirya ku tai makaranta na rasa zaman uwarwa kike a gidan nan da kika daina zuwa makarantar ja'ira Allah yasa su zaneki tas can. Ya juya tana masifar idan ta dawo ta iske su sai ta bugesu, harta koma ɗakinta tana masifa da tujara abin da yasa Malam ɗin fitowa daga ɗakinsa yayi mata magana "Haba Huraira daga samun sauƙinki zaki fara uzzura mata ko ? To wallahi ki kiyaye ba zan sake lamuntar abin da kike mata ba. Ai sai tayo waje kai buɗe tana jijjiga jikinta tana taɓa hannuwa tana cewa "Kasan Allah Malam da gaske nake kan yarinyar can sai munyi ruwan rashin arziki da kai ?To kama saurara kaji na rantse da Allah sai in bata kashi inga in zaka iya hanani" ya dubeta ya girgiza kai ya wuce yana "Allah ya baki lafiya Huraira lamarinki akwai firgicewa wallahi" ya leƙa ya iske har sun shirya fuskar Bilkisu kawai ya kalla yaga yanda taci kuka ga damuwa kwance akan fuskar yace "Yar albarka kiyi haƙuri da yanayin rayuwa wata rana sai labari, duk wanda ya ɗan ɗani ɗaci tabbas zai ɗan ɗani zuma kinji ? Kai ta ɗaga masa hawaye na shirin sake zubo mata ta kauda kanta, ta kama ƙannenta suka wuce islamiyar.

MAMAYAWhere stories live. Discover now