Season Eleven

74 10 0
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
  *RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR*✍️
              _Nafisat Isma'il Lawal Goma_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________📗

        *SEASON ELEVEN*

_______📖"Katabbatar sun nuna maka takardun motan su kafin su wuce". Yafaɗa maganar yana kallon Jone fuska a ɗaure

"Ok sir". Jone yafaɗa yana me sara masa

Juyawa yayi kawai yatafi cikin tafiyan sa na zaratan maza yabar wajen


Lumshe idanun ta tayi tana sake kwantar da kanta jikin kujeran, tana jin sanda Jone yake sake tambayan Ramcy numban wayan ta, kuma tana jin sanda yayi musu sallama har yana ce mata

"Baby baza ki buɗe idanun ki muyi ban kwana ba?"

Buɗe idanun kuwa tayi sai dai bata kalle sa ba tayi wa motan keey taja da wani irin Speed tabar wajen

Gaba ɗaya sojojin sake kallon motan sukayi suna jinjina ƙarfin hali irin na RAUDHA, tabbas ko basu faɗa ba akwai abinda tataka har take iya yin hakan agaban su

Shima ɗin idanun sa kawai yazuba ma motan cike da mamakin tantiranci irin na yarinyan da har take musu tsaurin ido, har motan taɓace ma ganin sa kafin yadena kallon hanyan. Ahankali yasauke ɓoyayyen ajiyan zuciya yana me lumshe idanun sa cike da tuno suffarta, murmushin sa me kyau yasaki yana ɗaukan wayan sa dake faman ƙara yakanga a kunne bayan yayi peacking call ɗin.



          🌐🌐🌐

Har suka shiga cikin Kaduna babu wanda ke magana cikin su

Akaro na biyu RAUDHA tasake kallon Ramcy da har yanzu bata dawo dai-dai ba, juya kanta tayi kafin tasake maimaita tambayan da tayi mata

"Ramcy tunanin me kike yi ne ina tambayan ki ina muka dosa?"

Sai alokacin Ramcy tadawo hayyacin ta sosai, cikin jan numfashi tace "uhmm Besty wlh ban ji ba duk hankalina ya tashi da ganin wannan dogon mutumin me murɗaɗɗen jiki, nayi tunanin yau kashin mu ya bushe wlh, don nasan halin sojoji basu da mutunci ko kaɗan".

Siririn tsaki RAUDHA taja batare da tace uffan ba taci gaba da sharara gudu

Ganin haka yasa Ramcy tasoma nuna mata inda zasu yi

A ƙofar wani madaidaicin gida suka tsaya, gidan me dakali ne da yasha suminti tare da sabon penti, koda gani ansan cewa gidan ana sha'ani sabida yanda mutane maza  da mata suka cika ƙofar gidan, da alamun dai wani wajen Za'a tafi don gefe ɗaya motoci ne sun fi biyar afake

Tunda motan tatsaya yawancin mutanen wajen sai idanuwan su yadawo wajajen

Sun ɗau lokaci kafin Ramcy tasoma fitowa, sai da tafito taleƙa da kanta tana kallon RAUDHA da bata da alamun fitowa tace

"My Besty don Allah fito mushiga kiyi haƙuri".

Yamutsa fuska RAUDHA tayi tana sake kallon mutanen wajen ta cikin motan, cikin ƙare musu kallo da taɓara tace "kinsan bana Son mutane idan nafita kallona zasu riƙa yi".

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now