Season Fifty

86 13 8
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.

            *HADHISI*
_An karbo dga Aisha Allah yqara yarda agareta tace " Manzon Allah s.a.w ya aureta tana da shekara shidda,kuma yatare da ita tana da shekara Tara,kuma Allah ya karbi ransa tana er shekara sha takwas.
Muslim ya ruwaito_

.

*NOT EDITED* ___________________________📗

*SEASON FIFTY*

_______📖 Washe gari RAUDHA ta haɗa Trollyn kayan ta ta wuce gidan su Ramcy, a ranan ma suka koma gidan RAUDHAN, ita da Ramcy da wasu tsirarun ƙawayen ta calss mate ɗin ta da suka zo mata biki, acan za su zauna ayi mata gyaran jiki da RAUDHA zata ɗau nauyi, da duk wasu shirye-shirye da ya kamata su yi

Duk a ranan ne dai me gyaran jikin ta iso aka soma wa Ramcy gyaran jiki, su kuma su RAUDHA da sauran ƙawayen su ne masu fita suyo abubuwan buƙata, duk a motan RAUDHA ake fita, duk da su ma ƴan matan ƴaƴan masu shi ne, wasu ma aciki da motan su suka zo, ga su suna da iyayi irin na gogaggun ƴan bokon nan ƴaƴan masu hannu da shuni, amma tunda suka ga RAUDHA sai suka raina kan su, ko wacce cikin su tana so ta shige mata

Ita kuwa ko kallo basu ishe ta ba, idan ma tana son yin abu, sai dai ta tambayi Ramcy, ita kuma Ramcy sai ta haɗa ta dasu su taimaka mata, shiyasa suke fita tare, ahaka har suka soma shige mata tana kula su, shima sai su ne suka tsulmo ta cikin zancen su

Itama RAUDHA har da ita akayi mata gyaran jikin kaɗan, ta ma ce ba ta so but Ramcy sai da tasaka akayi mata

Komi sun shirya agidan, inda suka koma gidan Aunty Nafeesa ana gobe bikin, don acan za su yi taron su na ƙawaye.

      Gidan su Ramcy ya cika maƙil da mutane, domin babu laifi suna da dangi sosai, musamman dangin Mahaifiyar ta, su ma sun zo da yawa, duk da ba Mahaifiyar a raye amma sun yi mata kara sosai, haka zalika Amaryar Baban su ma tayi gayya sosai, tunda ita a wurin ta ta riƙe su Ramcy tamkar ƴaƴan ta ne, sai kuma dangin Mahaifin ta, duk da su anan Zarian suke ma.

      Doctor Salman sunan Mijin da Ramcy zata aura, anan Zarian yake, a cikin samaru, babu laifi suna da hali sosai, don zan iya cewa ma, duk a cikin ƴan uwan sa ya fi su samun kuɗi, lokacin da Ramcy take zuwa A.B.U Zaria suka haɗu dashi, inda shi kuma ya je karantar wani course, kamar da wasa dai abun nasu, domin ita Ramcy taƙi ba shi damar yaga gidan su ma, a school kawai suke haɗuwa su gaisa, har ma sun rabu daga baya, tunda shi shekara ɗaya kacal yayi a lokacin. Sai kuma watarana kwatsam ya zo anguwan su wajen wani abokin sa, suka sake haɗuwa ita kuma ta fito gidan Aunty Nafeesa, anan yake faɗa wa abokin nasa "ita ce wacce ya so ta bashi dama taƙi" shine abokin yace "ai kuwa ga gidan su can idan kana so in Kai ka, ai Yayan ta Aboki na ne, Lawan".

"Haba dai kana nufin Lawan Jaga?"

"Shi fa". Abokin nasa ya sake tabbatar masa

Da wannan hiran nasu Salman yace, "ai kuwa zai sake dawowa, dama gida an matsa mishi ya fito da mata, shi kuma be shirya auren zumunci ba, kawai shi Ramcy ɗin ce tayi masa a yanzu, bari ya koma ya gwada sa'ar sa".

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now