Forty Nine

70 9 1
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.

.

*NOT EDITED* ___________________________📗

*SEASON FORTY NINE*

_______📖 Sosai Ray yake tsotson bakin ta tamkar ya samu Lolipop, ko kaɗan yaƙi bata damar da zata iya ƙwatan kanta, duk da kuwa kici-kicin da take yi domin gujewa abinda yake mata

Sosai ta gaji dole ta ƙyale shi ta dena ƙoƙarin ƙwace kanta, sai kawai ta soma zubar da hawaye tana sauraron saƙon da yake bata, rufe ido kawai tayi zuciyar ta na ƙara cinkushe wa da tsanar sa

Ray sai da yaga ya kusa losing control ɗin sa, kafin yayi ƙarfin halin sakar mata bakin ta yana me ja baya a hankali cike da kasala

Kallon ta kawai yake yi yanda ta tsaya tana ta kwararan hawaye idanun ta arufe

"Daga yau ki sake yi min rashin kunya, tara ki nake yi dama, kuma duk zan fanshe, idan hakan ta sake faruwa a tsakanin mu, to ba iya nan zan tsaya ba, don dai Ni ina da tsoron Allah ne ba irin ki ba".

Juya wa yayi ya wuce ƙofa zai fice

A lokacin ne ta buɗe jajayen idanuwan ta tana kallon sa, cikin ƙunan zuciya tace, "har abada bazan taɓa yafe maka ba, na matuƙar tsanar ka fiye da mutuwa ta, komi da komi dake tare da kai ba na ƙaunar sa, MAHAUKACI KAWAI". Taƙare maganar cikin ɗaga murya, don ba kaɗan ba kalaman sa suka yi mata ciwo

Be ce mata komi ba, illa murmusawa da yayi ya buɗe ƙofan yana shirin fita

Hakan sai ya ƙara mata zafi a zuciya, domin so take yi ta ƙuntata masa kafin ya bar ɗakin, cikin tsanar sa tace, "Mutanen kirki ba sa nuna kansu, sai dai ayyukan su su bayyana su, kai ko kaɗan ba ka a cikin su, domin ayyukan ka tuni sun bayyana min kai tantirin ɗan iska ne, masu fake wa a cikin mutanen kirki, alhanin irin ku su ne ɓatattu".

Sosai kausasan kalaman ta suka taɓa sa, juyo wa yayi yana kallon ta ido cikin ido, sun ɗau two minutes suna aika wa junan su kallo, kafin ya tako ahankali zuwa wajen ta, har yanzu kuma idanun su na a cikin juna, sai da ya tsaya gaban ta kafin yace, "kina bani mamaki RAUDHA, idan kina yin wani abu sai in ga tamkar baki da wayau, koda yake har yanzu ke yarinya ce, amma kuma ina me miki nasiha ki zama na gari a duk inda kike, har yanzu da sauran ki a cikin rayuwar nan, abu ɗaya yake hana Ni faɗa miki kalaman da zaki dauwama kina me dana-sani, dana-sanin rayuwar ki, amma kuma.."

Sai yayi murmushi yana fito da harshen sa waje, ya karkaɗa sa yana cewa, "amsa ɗaya nake so ki bani, ɗaya tak. Da Ni da ke ina son sanin waye ɗan iska?".

Sai yayi dariya yace, "ba ma sai kin bani amsa ba shalele na, Ni ai ƙaramin ƙwaro ne a iskancin domin ban san komi ba, ke kuwa da, Kin dauwama ne a cikin ta tun kina ƙaramar ki, ga shi har yanzu kin kasa gane Allah ya faku bare ki tuba, ko ba ke ce na kama ki jiyan nan da ƙani na kuna abinda kika saba ba? To ki soma gyara kanki kafin ki ce zaki zagi wani".

Juya wa kawai yayi ya bar ɗakin batare da ya jira cewar ta ba, yana fita ya zauna kan sofa a parlour, yana me ɗaura kansa jikin kujeran tare da lusmshe idanu

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now