Season Twenty One

54 10 0
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
  *RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR*✍️
              _Nafisat Isma'il Lawal Goma_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________📗

        *SEASON TWENTY ONE*

_______📖 Direct wani gida suka nufa me kamar kango amma da akwai Gate a gidan, suna shigar da motan suka fito da ita, su uku ne mazan yayinda ɗaya ne yaɗauke ta yasaɓa ta a kafaɗa suka nufi cikin gidan da ko ƙofofi babu sai window

Kamar mintuna biyar da shigan su sai gidan yasoma amsawa da wani irin kuka me ban tsoro haɗe da wani irin gurnani tamkar za'a fasa gidan, kukan sosai yake ƙaruwa sai kuma yahaɗe na mutane da yawa wanda baza ka iya gane na aljanu bane ko na mutane, zuwa can kuma sai kukan yalafa sai ga RAUDHA ta fito tana layi gashin kanta duk ya barbaje ya rufe mata fuska, duk da dare ne but bazai hana ka hango yanda idanuwan ta ke wani irin walƙiya ba tamkar yanda na mage yake yi idan tafito da dare, tafiya kawai take yi har tafice cikin gidan tadoshi cikin daji, duk da dama gidan a wajen gari yake

Sai da tayi tafiya me nisa kafin tafaɗi ƙasa yashe babu alamun numfashi a tattare da ita.

         🌐🌐🌐🌐🌐🌐🌐

      Washe gari har Suhaib yashirya zuwa Office yana jiran dawowar RAUDHA amma babu ita, duk da yasan bata kai wa har safiya idan tafita but yayi tunanin ko tana can ɗin ne inda tasaba zuwa, jin shiru bata dawo ba sai yatafi Office

Koda yadawo Farida ta tabbatar masa bata dawo gidan ba sai hankalin sa yayi mugun tashi, wayanta yasoma kira duk da kiran ya shiga but babu answer, sai da yayi Three missed calls kafin Rash taɗaga Kiran, tunda dama a motan Zen RAUDHA tabar jakan ta, su ma sun shiga tashin hankali musamman da suka neme ta suka rasa, daga baya kuma sai suka yi tunanin ta wuce gida ne duk da sun ji haushi sosai Zen da Maan tunda sun yi tanadin ranan sosai akanta, amma tatafi tabar su

Abinda yasoma fita a bakin Suhaib sanda Rash taɗau wayan shine "Baby Ina kika je har yanzu baki dawo gida ba kin ɗaga min hankali sosai?".

Jin hakan sai Rash ta tabbatar akwai matsala, itama cikin tashin hankali da yanuna a muryan ta tace, "Ba RAUDHA bace ƙawarta ce, ta bar jakarta ne a wajena kuma naga kana kira".

Suhaib dake zaune be san sanda yayi zumbur yamiƙe ba

"Whattt... Ki kace mene? Ita ina taje ne da tabar wayan a hannun ki?".

Cikin tsoro Rash tabashi amsa da yanda aka yi su ma suka neme ta suka rasa

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un". Abinda Suhaib yafaɗa kenan yana me sakin wayan a ƙasa

Lokaci ɗaya zufa ya tsatstsafo masa a saman goshi, ga wani irin jiri da yamamaye sa nan take sabida tsananin tashin hankalin da yaziyarce sa

Farida dake zaune da ciki a gaba tana tambayan sa "meke faruwa?" Be ma san tana yi ba

Sai da yayi good 5 minutes a gushewar tunani kafin yadawo dai-dai, lokacin kuwa tuni hawaye sun ciko masa idanu yakalli Farida da tamiƙe tsaye itama hankalin nata a tashe, cikin raunin murya yace

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now