Season Twenty Two

69 12 1
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
  *RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR*✍️
              _Nafisat Isma'il Lawal Goma_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

.

  *NOT EDITED* ___________________________📗

        *SEASON TWENTY TWO*

_______📖 RAUDHA bata farka ba har washe gari

Wajen ƙarfe 07:00am. Wani magidanci yazo wuce wa yahange ta, da farko ya ji tsoro sai dai kuma yayi shahada wajen ƙarisawa wajen ta, hannu yakai yana taɓa ta sai dai ko kaɗan babu alamun numfashi a tattare da ita, sai da yasake kai hannun sa setting hancin ta nan ma be ji komi ba, sai yariƙe tsintsiyan hannun ta anan ne yatabbatar tana da sauran rai, ajiye fatanyan sa yayi yaɗago ta yasaɓa a kafaɗa sannan yayi hanyan gida

Kasancewar safiya ne mutane duk suna gida basu kai ga fitowa ba, don haka har yakai gida be haɗu da kowa ba duk da babu nisa sosai da rugan da suke

Yana shiga yasoma ƙwala wa matar sa kira

Da gudu Lantana tafito tana aza ɗankwalin ta kanta at the same time tana amsa mishi da faɗin "Malam lafiya..?"

Sai dai bata iya ƙarisa maganar ba ganin sa saɓe da RAUDHA a kafaɗa

"Tukunna dai ɗauko min Tabarma sai in miki bayani ko?"

Lantana ta'amsa mishi dasauri tana shigewa ɗaki taɗauko tabarman kamar yanda ya umarce ta, shimfiɗa wa tayi sannan yasauke RAUDHAN akan tabarman

"Malam wannan yarinyan daga ina, aina kasamo ta?" Lantana tayi masa tambayan lokacin da tasami waje tazauna tana kallon sa

"To nima dai ga tanan tsintan ta nayi cikin jeji, ganin tana numfashi shine nataimaka nakawo ta nan".

"To Malam me zai saka kakawo mana ita nan bayan gidan me Gari zaka kai ta? Mu kuma me zamu yi mata?"

Ɗan sauke numfashi Malam Umaru yayi kafin yace, "to nayi tunanin hakan nima ai, sai kuma na tuna ɗazu da asuba da muka yi sallah me Gari ya sanar mana zai yi tafiya a lokacin, har yake neman addu'ar mu shiyasa nayi tunanin kawo ta nan ɗin tunda ko an kaita can babu me kula da ita".

Lantana da idanun ta suka ƙi ɗauke wa akan RAUDHA tasake cewa, "Malam nifa wlh ina jin tsoro, yarinyan fa ko motsi bata yi yanzu mu wani taimako zamu bata? Kai da ganin yarinyan nan kasan ƴar cikin birni ce, asibiti Ya kamata a kai ta, kar mu zo Garin taimako mu afka cikin matsala, idan ka kaita can sai kayi musu bayanin tsintan ta kayi kaga sai su nemi ƴan uwanta tunda su ƴan birnin sun san yanda zasu yi su same su".

Kallon Lantanan yayi yace, "ke kina ganin haka kawai zan kai ta asibiti baza su caje Ni kuɗi ba? Dole sai mun biya kuɗi kuma kinsan ban da komi a yanzu, sannan wannan yaron ban san ranan dawowar sa ba da sai yataimaka mana, amma Ni abinda naga ya dace ki je gidan Jummai me magani tazo taduba ta sai aga abunda hali zai yi, kinga idan muka samu tafarfaɗo sai tafaɗa mana inda take mu maida ita, kinsan be kamata mu bar ta bamu taimaka mata ba domin tana buƙatar taimakon, Allah yaga zuciyar mu zai bamu nasara, ko sada ta muka yi da ƴan uwan ta zamu samu lada".

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now