Season Fifty Five

192 16 0
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.

.

*NOT EDITED* ___________________________📗

*SEASON FIFTY FIVE*

_______📖 Zan iya cewa komi na gidan nan ɗaya yake da wancan, sai dai banbancin colour da kuma haɗuwa, amma tsadan su ɗaya, wannan dai ya fi haɗuwa sosai, akasarin komi fari aka saka mata shiyasa yafi ɗaukar ido da burge wa.

      A gajiye suka shigo gidan, don haka sallah suka soma gabatar wa na azahar da asar, sannan Ray ya aiki Drever'n sa don ya yo musu take-away, kafin ma ya dawo har RAUDHA ta soma barci, sabida ba ƙaramin barci take ji ba

Tashin ta yayi yace, "ta zo su ci abinci".

Daƙyar ta tashi tana ɓata fuska, gaba ɗaya tayi yaushi sabida barcin ya rufe mata ido, zama tayi gefen gadon, ta dafe gadon da hannayen ta tana me lumshe idanun ta

Ahaka Ray ya fito daga Toilet ya sake tarar da ita har barci ya soma ɗaukar ta, ruwan hannun sa ya yarfa mata yana me faɗin, "Baby wake-up mana".

Buɗe ido tayi ta ɗan kalle sa kaɗan da idanun ta da suka sauya kala, sai ta ɓata fuska tace, "Ka bar Ni inyi barcin don Allah, ba na jin yunwa".

"Ban yarda ba, ke dai kawai ki ce barci kike ji, amma ba wai ki ce ba kya jin yunwa ba. miƙe kin ga idan kin ci sai ki koma ko?" Yayi maganar yana me lallaɓa ta

Turo baki tayi tana sosa kanta, sai kuma ta miƙe tana nufan ƙofan zata fice

Riƙe ta yayi suka fita Parlour, ya zaunar da ita saman kujera, sannan ya wuce kichen don ɗauko Plate

Jingina tayi da jikin kujeran tana me lumshe idanun ta, har ya dawo ya sake abincin bata motsa ba, shi da kansa ya bata abincin tunda ta ƙi ci, yana ta faman lallaɓa ta, sai daga baya ne ta Ware sosai taci tunda tana jin yunwa

Sai da suka gama yace mata "ta koma ta kwanta, shima fita zai yi".

Bedroom ta koma ta kwanta akan gado, babu jima wa barci ya ɗauke ta

Shi kuma sai da yayi wanka ya shirya cikin manyan kaya, gezna ne me ruwan kore, amma Light ne, ta sha aiki sosai har da babban rigan ta, sai dai be saka babban rigan ba, ya murza hulan sa mu haɗu a banki, sannan ya feshe ko ina nasa da turaruka, sak ya fito a Angon sa sai ƙyalli yake yi, fuskar sa na fid da annuri, keey ɗin mota ya ɗauka tare da wayan sa, ya matso gadon yayi mata kiss a leɓen ta, sannan ya shafa kanta yana murmushi a ransa yana aiyana abubuwa da dama. Fita yayi ya hau motan sa ya nufi gidan su RAUDHA

A can ya wuni wajen Daddy, har magriba be dawo ba, sai da RAUDHA ta kira sa tana masa shagwaɓan "ya bar ta ita kaɗai" sannan ne yayi haraman taho wa, da zai dawo sai da ya biya ya siya kazan amarcin sa, don yau so yake yi ya zama cikakken Angon sa

Da fara'an sa ya shigo gidan, inda ta tarbe sa tana me rungume sa tana faɗa masa "how much she missed him" kafin ta amsa kayan hannun sa tana me ƙara masa sannu da zuwa har da duƙawa alamun girmamawa

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now