Forty Four

79 10 0
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
      *RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR:* ✍️
              _Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
                     2021.

.

  *NOT EDITED* ___________________________📗

        *SEASON FORTY FOUR*

_______📖 Daddy ya saka ana ta shirye-shiryen tarban iyayen Rayyan da za su zo, an gyara musu ɗakunan ƙasa da ba a amfani da su, duk wani abubuwan jin daɗi ya saka an zuba musu

Alh. Hassan da suke kiran sa da Uncle Hassan, shine Abokin Daddy. Asalin Abotan su ya fara ne sanda Daddy yayi zaman Bayelsa yin wani course, to anan suka haɗu da Uncle Hassan Wanda gaba ɗaya ahalin su sunan da suke kiran sa da shi kenan, tun yana ƙarami, kasancewar sunan Kawun sa shima ya ci, to lokacin da aka haife sa a lokacin ne Kawun nasu ya rasu, shiyasa da aka mayar da sunan Kawun shi ne suke kiran sa da Uncle Hassan kamar yanda suke kiran Kawun, har Allah yasa ya girma da sunan ake kiran sa, yanzu haka har iyalan sa duk Uncle suke kiran sa, su Rayyan ba sa kiran sa da Baba sai dai Uncle.

      Kasancewar Daddy yana yawan zuwa gidan su Uncle Hassan, anan kusa da gidan su ya haɗu da mahaifiyar su RAUDHA, suna maƙotaka ne da gidan su Uncle Hassan, inda babu ɓata lokaci soyayya me ƙarfi ya shiga tsakanin su, koda ya tashi aure sai Allah yasa ita ɗin rabon sa ne, a time ɗin iyayen sa suna raye, har can suka je nema masa auren Ruƙayyah, inda aka ba shi babu wani ja'inja

    Anan Zaria suka soma zama, cikin ƙofan doka, Allah da ikon sa rayuwa taci gaba da gudana, inda a gefe ɗaya suna Abotan su sosai da Uncle Hassan, shima be daɗe ba yayi aure a can Bayelsa

Babu jima wa Matan nasu suka haihu a tare, inda yaran suka ci sunan Rayyan da Suhaib. Haka rayuwa taci gaba da gudana, Ruƙayya dai bata sake haihuwa ba, sai matar Uncle Hassan Hansa'u da ta haifi Umar Faruk, suna kiran sa da Faruk tunda sunan mahaifin ta ne, wani lokacin kuma su kira sa da Abba, daga shi kuma sai Usman da suke kiran sa da Zannurain, sai kuma  Abubakar autan su, shi ne sa'an RAUDHA, an haife shi babu daɗe wa aka haifi RAUDHA, shekarun ta biyar a duniya Ruƙayya ta rasu a wajen haihuwar ƙanwar ta, lokacin tana cikin naƙuda, domin har ta kusa haihuwa, da ita da abun da ke cikin ta gaba ɗaya suka koma ga Allah saboda ta sha wahala a lokacin. Wannan dalilin ne Daddy da Suhaib suka ɗauki son duniya suka aza wa RAUDHA, ga tsaban tausayin ta da suke ji.

          🌐🌐🌐

      Drever yaje ya ɗauko su a airport sanda suka sauka, suna iso wa Uncle da Daddy suka rungume juna, ko wannen su cike da farin cikin ganin Abokin sa, domin sun jima rabon da su haɗu sai yanzu, shiyasa Uncle Hassan ya shirya zuwa gaba ɗaya har iyalan sa

Sai da suka daɗe suna gaisa wa cike da barkwanci kafin suka samu wuri suka zauna, inda su Faruk ɗaya bayan ɗaya suka hau gaishe shi. Ya amsa musu cike da fara'a yana tambayan su school da aikin su. Sannan suka gaisa da Ammee cikin mutunci

Uncle ne ya soma tambayan RAUDHA, kasancewar shi kaɗai ya san ta, ita kanta Ammee tun tana yarinya rabon da ta sake ganin ta

Daddy na murmushi yace, "yanzun nan zata dawo, ta je gidan ƙawar ta ne (Ramcy)".

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now