Season Fifty Two

77 14 3
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
*RAUDHA*
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

*MALLAKAR:* ✍️
_Nafisat Ismail Lawal Goma._

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO*📖
'''®Ɗaya tamkar da Dubu'''💪✓

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattapad: UmmuDahirah*👈

*\F.W.A📚/*

*RAMADHAN MUBARAKH*🤲🏽🕌
2021.

.

*NOT EDITED* ___________________________📗

*SEASON FIFTY TWO*

_______📖 Hannun ta ta zame daga na Daddy, ta tashi da gudu tabar ɗakin tana sake rushe wa da wani sabon kukan

Daga Daddy har Ray dake hawaye bin ta suka yi da idanu har ta fice

Daddy sosai jikin sa ya sake sanyi matuƙa, har ya kasa ma yin magana, illa shiru da yayi yana afka wa duniyar tunani

While Ray, shima ya kasa koda jirga wa ne, illa lumshe idanuwan sa da yayi yana sauraron bugun zuciyar sa da ya sauya, ba ya jin zai iya jure rashin RAUDHA a tare dashi, yana matuƙar ƙaunar ta, ya rigada ya saka ta can cikin zuciyar sa, kuma fitan ta zai yi wuya a gare sa, tabbas yana ji a jikin sa muddin ya rasa ta zai iya shiga wani hali, shi kansa be san iya adadin ƙaunar da yake mata ba, kuma be san meyasaka soyayya tayi masa muguwar kamun nan ba..

    Muryan Daddy shi ya katse masa tunanin sa, yace mishi "ya je insha Allahu idan RAUDHA rabon sa ne, zai same ta, shi kansa yana goyan bayan ya kasance miji a gare ta".

Sosai Daddy ya ƙara masa ƙwarin gwiwa, kuma ya ce mishi ya dage wajen bata haƙuri, insha Allahu shi ke da nasara, shima zai taya sa roƙon ta

    Rayyan yaji daɗin kalaman Daddy, haka yayi masa sallama ya wuce Kaduna, sai dai a ƙasan zuciyar sa tunanin RAUDHA ne maƙil, amma babu yanda zai iya tunda yasan hakan sai ya faru.

              🔵🔵🔵

    Fannin RAUDHA kuwa abu yayi tsamari, gaba ɗaya ta hana kanta sukuni, ko kaɗan taƙi sauraren Daddy da maganar, da ya faro zancen zata soma mishi kuka akan "ba ta son sake jin maganar Rayyan". A cikin kwana biyu sai gata ta zabge sosai sabida damuwar da ta saka wa kanta, sosai take wahaltuwa da rashin Ƙalby ɗin ta, ita kanta ta san zai yi wuya ta jure rashin sa, tana mishi mahaukacin son da baki ma bazai iya fasalta shi ba, soyayyar sa ya rigada yabi jinin jikin ta, duk yanda ta so ta manta shi a ranta, ta cire sa ta goge sa gaba ɗaya a babin rayuwan ta, tayi rayuwa tamkar ma bata taɓa sanin sa ba ta kasa, dole ciwo ya kwantar da ita

Daddy gaba ɗaya hankalin sa ya tashi sosai, tausayin ɗiyar sa ya cika masa zuciya, sai dai taurin kanta yasa tana wahalar da kanta bayan tana da maganin matsalan ta, Doctor ya samo mace tana kula da ita a gida, da abun yayi tsamari dole aka wuce da ita asibiti, abu kamar wasa sai ga RAUDHA magashiyan tana jinya me tsanani har da su ƙarin ruwa, damuwar da ta saka a ranta ya haifar mata da ciwo me tsanani

Dole Daddy ya kira Suhaib ya sanar masa da komi, a ranan sai ga shi ya iso, sosai hankalin sa ya tashi ganin ƙanwar sa ta rame matuƙa, tausayin ta sosai ya kama shi, ba ma ita kaɗai ba har Rayyan, domin yasan cewa shima yana cikin wani hali koda be sani ba, tun farko ya gane Rayyan na ƙaunar ta, amma be taɓa tunanin shi ke bibiyan ta har suke wannan soyayyan ba, Allah Sarki Rayyan, ya so kiran sa ya sanar masa abinda ke faruwa da RAUDHAN, sai kuma yaga wani sabon tashin hankalin ne zai ɗaura masa, dole ya zauna rarrashin ƙanwar tasa, yana faɗa mata "ta amince da Rayyan, ta yafe masa domin samun kwanciyar hankalin su gaba ɗaya, domin yasan cewa shima yana nan cikin tashin hankali fiye da yanda take ciki".

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now