Season Twenty Seven

66 9 0
                                    

🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂
🐾🐾🐾🐾🐾
🍇🍇🍇🍇🍇
   𝐑𝐀𝐔𝐃𝐇𝐀
🍇🍇🍇🍇🍇
🐾🐾🐾🐾🐾
🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂🍂

𝐌𝐀𝐋𝐋𝐀𝐊𝐀𝐑: ✍️
              𝑁𝑎𝑓𝑖𝑠𝑎𝑡 𝐼𝑠𝑚𝑎'𝑖𝑙 𝐿𝑎𝑤𝑎𝑙 𝐺𝑜𝑚𝑎.

*بسم الله الرحمن الرحيم*


𝐅𝐄𝐄𝐍𝐀𝐇 𝐖𝐑𝐈𝐓𝐄𝐑'𝐒 𝐀𝐒𝐒𝐎📖
®Ɗ𝚊𝚢𝚊 𝚝𝚊𝚖𝚔𝚊𝚛 𝚍𝚊 𝙳𝚞𝚋𝚞💪✓

𝗝𝗜𝗞𝗔𝗥 𝗟𝗔𝗪𝗔𝗟𝗜 𝗖𝗘✍️

𝗪𝗮𝘁𝘁𝗽𝗮𝗱: 𝗨𝗺𝗺𝘂𝗗𝗮𝗵𝗶𝗿𝗮𝗵👈

         \𝗙.𝗪.𝗔📚/

.

  𝗡𝗢𝗧 𝗘𝗗𝗜𝗧𝗘𝗗 ___________________________📗

        𝗦𝗘𝗔𝗦𝗢𝗡 𝗧𝗪𝗘𝗡𝗧𝗬 𝗦𝗘𝗩𝗘𝗡

_______📖 Farida ce tashigo ɗakin a rikice, sabida ihun RAUDHAN ne ya tashe ta daga barci shine ta hayo saman taga me ke faruwa

Dai-dai lokacin da Suhaib yake ƙoƙarin zuba mata ruwa a fuska, shima ɗin duk a rikece yake hankalin sa duk ya tashi

Da sauri taƙariso wajen gadon tana tambayan sa abinda ke faruwa

Be iya ce mata komi ba saboda hankalin sa na kan RAUDHA da ta kawo numfashi, sai dai bata buɗe idanu ba illa wani irin nannauyan barci da ya kwashe ta

Girgiza ta Suhaib ya soma yi yana kiran sunan ta, sai daga baya shima ya fahimci barci ne ya ɗauke ta, mamaki sosai ya cika sa da barcin nata, da sauri ya sake zuba mata ruwa ko wai zata farka, amma ko motsin kirki taƙi yi, ga dai shi numfashin ta na fita normal irin na masu barci amma taƙi farka wa

Farida dake tsaye kan su itama tana kallon RAUDHAN, duk hankalin ta ya gama tashi, sake tambayan sa tayi

Anan ne ya faɗa mata abinda ke faruwa, har zuwa suman da RAUDHA tayi, kafin yaja numfashi yana saka hannun sa a aljihu don ɗauko wayan sa ya kira doctor, domin dai hankalin sa ya gaza kwanciya da wannan barcin da RAUDHA ta kama a lokaci ƙanƙani

Shaf ya manta ma, yau be yi amfani da wayan sa ba, kuma a kashe ya barta tun jiya, wannan dalilin ne ma Daddy da ya kira sa be same sa ba, sai ya kira RAUDHA

Kallon Farida yayi yace, "Wifey ɗauko min wayana in kira Doctor, sabida hankalina ya gaza kwanciya da wannan barcin da Baby ta hau yi, anya ma barcin take yi?"


Umarnin sa Farida tabi, tafice da sauri taje ta ɗauko masa wayan

Kiran doctor yayi ya sanar masa da halin da ake ciki

Nan yayi masa alƙawarin zuwa nan ba da jima wa ba, tunda yau weekend ne yana gida.

Babu jima wa kuwa sai gashi yazo, duba RAUDHA ya hau yi, sai dai shima be gano komi dake damun ta ba illa barcin

Nan ya yi wa Suhaib bayani kafin yayi masa sallama ya fita

Sai alokacin ne hankalin Suhaib ɗin ya ɗan kwanta, rufe ta yayi da bargo sannan suka fito shi da Farida, a Parlour suka zauna zugum duk rai babu daɗi, musamman Suhaib da damuwar suka haɗu sukai mishi yawa, ga matsalan Daddy da be san ma ta ina zai soma ɓullo wa al'amarin ba, ga kuma halin da RAUDHA take ciki.

          A haka ranan suka wuni sukuku, har dare RAUDHA bata farka ba, hakan yasa hankalin Suhaib ya sake tashi, dole ya sake kiran wani doctor ɗin ya duba ta, shima ɗin be gano komi ba, barcin dai ya sake faɗa musu shi take yi

RAUDHA 2021Where stories live. Discover now