42=UKU-BALA'I

469 31 1
                                    

*******
Sunkoyawa yayi da zubar debo ruwa a gorarsa har ya nitsar da ita sosai yana kokarin dagowa yaji ta maƙale gabadaya taki daguwa hakan yayi matukar daure masa kai shiru yayi kamar mai tunani wani abu kafin ya sake dago gorar tasa amma ina! sai yaji kamar an kara daura mata gingimeman dutse.

"Ja'e zo ka taya ni gorata ta ki hidduwa daga ruwa".

Ja'e dake tsaye yana gabzar danyen Mangwaro ya juyo ya dube shi kafin yace.

"Ban fahimce ka ba me kake nufi?".

"Zo ka gani mana don Allah".

Ba tare da ya sake cewa komai ba ya tako zuwa wajen ya dube shi sannan ya dubi gorar da tayi kasa amma ga bakinta nan.

"Jayota mana kai ma sai kace wani sakakke ya za ayi gora ta makale a ruwa?".

Sake janyota yayi amma ina taki daguwa da karfin gaske ya fizgota gabadaya yayi baya ya zube a kasa gorar tayo waje sagale da ruwan rigar mutum hadi da kansa duk sunyo waje Ja'e dake tsaye bai san lokaci da ya kwala ihu ba ya ari na kare ya falle kamar wani zomo da yan farauta suka biyo shi Iro da ya baje cikin ciyayi mai taɓo ganin abin da Ja'e yayi ya tabbatar masa akwai abin da ya gani shima cikin tsorata da firgice ya k'urma da gudu shima ko tsayawa ganin abin da ke faruwa bai yi ba gudu ya shiga yi da yake irin siraran mutanan nan ne marasa jiki ga tsayi nan da nan ya kamo Ja'e da ke ta fama haki kamar wanda ya ɓalle daga lahira ya fado duniya.

Ba su tsaya tambayar juna ba suka sake arcewa gudu sukayi sosai har sai da suka fara hango bunkokin rugar su kafin su tsagaita suna mai da numfashi Ja'e ya sunkoya riƙe da kafafuwansa yana duban Iro da yake gabansa.

"Aradun Allah Iro lahira na hango".

Ya fadi yana mai waige-waige cikin tsananin firgici da razana Iro da yake can nesa dashi ya dube shi cikin rashin fahimta.

"Ban gane ba kaifa baka da hankali wa yace maka ana hango lahira daga nan duniya".

Nishi Ja'e ya saki na wahala kafin ya tashi tsaye sosai ya dubi bayansa sa'an nan yace.

"mutum ne fa kamar gawa na gani rike da Gorar...wai hala kai baka gani bane?".

Iro da yayi shiru yana sauraron Ja'e jin abin da yace ya sanya shi ware idanu waje.

"Aradu ban gani ba kawai biyo ka nayi don na tabbata abin da ka gani bala'i n...".

A guje suka sake kwasa suna zunduma ihu kamar wasu zararru sai faman tsalle-tsalle suke kawai don sun ji motsi abu cikin ciyayin da suke kusa da ita da wannan yanayin suka karasa cikin rugar ihun da suke ya firgita mutanan cikinta nan da nan kowa ya shiga kallon su ana tambayar dalili amma ba wanda yayi kokarin tsayawa balle ya basu ansar abin da ya jefa su cikin firgicin da suka samu kan su.

Da yake rugar ba mai girma bace kallo daya zakayi mata ka gane ZURI'A DAYA ce ta hadu a wajan don bunkokin na su tsilli tsilli suke a lissafe ba za su haura goma ba.

"Iro wai kalau kuke kuwa? Wannan wani irin wauta ne da girman ku da komai amma kuna wannan shiriritar".

Tsohon da suka gilma gindin wata bunka ya shiga fadin haka cikin yanayi na jin haushin abin da ya ga sunayi don mafiyawancin lokaci haka suke indai suka dawo kiwo sun dinga nuna yarintar su ke bayan kuma a shekaru ba wanda bai haura ashirin ba kuma ko wanne da matarsa ta aure.

UKU BALA'I (Completed)Tempat cerita menjadi hidup. Temukan sekarang