AUREN DOLE sabon salo
Part 24
Raqiyya benaMaryam tace anyi mami aike kin tuba kuma irin tubar da akeso bawa yayi insha Allah tubar ki ansashiya ce
Muci gaba da yi ma yaya Ahmad Addua kuma Allah ya shiryar dashi shima
Mami tayi shiruuuu
Wani zafi takejin yana ratsa ta
Ta durkusa tana maimaita kalmar innalillahi wa inna ilaihirraji'un
Da sauri maryam ra rike ta tana cewa lafiya anty? Ko haihuwa ce? Mami tace no this is my 8th month
Nan take jini ya fara zuba ai kuwa maryam ta sheka ta kira mummy
Da sauri aka dauki maryam zuwa asibity
Nan take aka shiga da ita labour room saboda premature labour ne ya kama ta
Har kusan awa biyar suna cikin labour room din sai can aka fito domin a saka hannu ayi mata CS
Dr Ahmad wanda duk ya gama rudewa ganin halin da mamin sa take ciki ya saka hannu don ayi mata CS a cire babyn su a ceto ran matar shi
Amma inaaaaa Mami rai yayi halin sa tun kafin a shiga da ita theater room
Ta rasu ba tare da ta haifi abinda ke cikin ta ba
Innalillahi wa inna ilaihirraji'un
Doctor ya fito ya sanar ma iyalan mami cewa Allah ya mata rasuwa, mutuwar zaune Ahmed yayi
Wani shock ne ya kama maryam nan take ta fadi wajen a sume
Suna fira lafiya dazu yanzu kawai ace mami ta mutu?
Dr Ahmad kam saida anka taba shi, juyawa yayi ya kalli Aish dake kwance a jikin fatima tana bacci hankali kwance
Jin yake kamar ya kuwwata, ya tuna lokacin da zai fito daga gidan da safe mami na zaune kan gado tana sanya ma Aish riga
Ya kalle ta yace mai ciki ayi sauri a haifo mana kayan mu, tayi dariya tace toh kuyi Adduar Allah ya kawo shi lafiya
Yayi dariya kawai ya ce toh amin, zan aiko a ansar min diyata idan na gama lecture na zuwa anjima
Tace toh ai gara ka aiko a dauke ta kar ta dame ni
Wani irin ihu Ahmad ya saki tare da faduwa kasa yana kuka kamar karamin yaro yana fadin maaaaaamiii
Karar da ya saki ce ta tayar da Aish daga bacci itama ta kama kuma daga ka gansu ka ga abin tausayi
YOU ARE READING
AUREN DOLE sabon Salo
Romancelabari ne me ban tausayi dakuma nuna cewa duk abinda Allah ya tsara ma mutun sai yafaru