Auren dole sabon salo
Part 33
Raqiyya benaA office din dr haidar maryam ta zauna kanta a kasa hawaye na zuba a idon ta
Dr yaja numfashi sannan yace ya kuke da patient dina?
Tace ex husband dina ne. ... a takaice tayi maganar
Kanshi ya daure don shi baima san ta taba aure ba
Yace do u love him? No kawai tace..
Yaja numfashi yace why are u here then? U r supposed to be celebrating your wedding by now
Ta danyi shiru sannan tace he is my brother gidan mu daya... daddynshi ne ma zai bada aure na
Kanshi ya kara daurewa
Yace well Dr this is about life and death
Maganar gskya its either ki auri Ahmad or sincerely we r going to loose him
Da sauri ta kalli dr
Yace yes kinga daga farkawa ya kara samun attack. Even now zai iya kara samun wani idan ya farka
We can't keep him unconscious forever kuma ko?
Ta dan numfasa tace I'll think about it kawai ta tashi ta wuce
San batajin tana son auren Ahmad again
Nan ta fara tuna aurenta dashi
First night dinsu wata ya kawo yayi zinah da ita a gidan
Ya auri mata har biyu bayan ita
Tana shekaru bata ganshi ba sam baya tuna yanada wata mata wai ita maryam
Ta numfasa bayan ta tuna yadda ya sake ta ta waya bayan sun kusan shekara biyu basu hadu ba a lokacin
Saida ya ganta yaga ta cika mace zaice yana son ta? Soyayya ko shaawa?
Lokaci daya kuna ta tuna da mummy
Gabanta ya fadi rasss
A ranta tace nasan duk son da mummy take min tafi son yaya Ahmad akaina don shine ta haifa
Idan har ban masu halaccin ceto dansu ba shekaru biyar da suka yi suna bani ingantaciyar rayuwa miye zata saka masu dashi ?
Indai yaya Ahmad ya mutu akan ban aureshi ba wallahi su daddy zasu daina so na ne
Gara ma mummy amma na san yadda daddy ke mugun son yaya Ahmad
Nabeel ta tuna da yaranshi sai kuma ta fashe da kuka
Kanta yayi zafi ta rasa dawa zatayi shawara
Amal ce kawai yar uwarta ta jini a duniya wadda take iya gayama irin wannan matsalar a yanxu don haka ta kira ta tace sister i need your help please
Gida ta nufa ta daura alwala tayi sallah tayi nafila sannan ta roki Allah ya zaba mata abinda yafi alheri a rayuwar ta
Ta dan samu natsuwa kadan sannan ta zauna taci abincin dare
Kusan karfe sha biyu ne lokacin don haka tana gamawa kwanciya kawai tayi
Misalin 9am ta tashi bayan ta koma sallar asuba
Ko 20mints batayi da tashi ba dai ga amal tazo
Suka zauna neman mafita
Amal tace sister gskya yakamata yayi ki auri yaya Ahmad don shine kawai abinda zakiyi ki dan saka ma iyayenshi da yan uwanshi soyayyar da suka baki tsawon shekaru
Ki duba komai baku hada ba na jini haka suka aura ma dansu baya so
Suka rike ki duk shekarun nan suka baki ilimi. Sukayi fushi da dansu akanki
Haba karma kiyi tunanin wani nabeel yaushe kika sanshi? Bakida kamar mummy da daddy a duniyar nan hadda mu da muke yan uwanki kuwa
Ki daure ki faranta masu rai maryam
Tabbas maryam ta san batada kaman mummy da daddy sukuma basuda kaman Ahmad don haka ta yanke shawarar auren Ahmad
Ta kira nabeel tace tana son ganin shi
Nabeel shima tunda yaji abinda yake faruwa yayi niyyan bata shawara su hakura da juna ta auri Ahmad domin yima mahaifan shi hallacci
Taji dadin yadda ya anshi maganar ta kuma yamata addua
Saide ya roke ta akan ta hada shi da amal idan akwai dama domin yaran shi yaga sun shaku da ita
Yana son ya samar ma yaranshi uwa ta gari
Taji dadin maganar dukda ita kanta tasan tana son nabeel tayi ma amal murna kuwa idan ta samu nabeel domin namiji ne mai kirki da sanin yakamata
A ranta tace halin amal na kwarai ne dole ta samu miji kaman nabeel
Sai kuma wata zuciyar tace ke halinki na banza ne da kika samu irin Ahmad? Kowa dai da qaddarar rayuwar shi
A dakin daddy...
Wallahil azeem saide a bayan raina zan aurar da maryam ga wani bayan Ahmad
Mummy tace haba alhaji ita shin maryam kayan wasa ce da zamu rinka wasa da rayuwar ta? Mutun ce kaman kowa
Shekara nawa tana zaune da ahmad a rayuwar kunci
Ganin kake duk gatan da muka bata yakai wanda mijinta zai bata amma ahmad ya zauna zinace zinace da walakanta ta
Haba alhaji na karka bata rawarka da tsalle mana
Ladar da muka samu wajen ceto rayuwar maryam zata lallace idan muka ce sai mun aura mata Ahmad dole yanzu
Munyi mata auren dole a karo na farko don Allah ka batta ta auri wanda takesoKo ta auri ahmad indai kwanan shi ya kare to tabbas sai ya mutu
Ribar me zamu samu idan muka tilasta ta komawa inda ta fito? Haba alhaji na
Jikin daddy ya dan yi sanyi amma sam baijin zai iya daura auren maryam da wani don haka yace shikenan hajiya ba damuwa maryam ta auri duk wanda takeso amma zan kira kawunta ya daura mata aure nidai bazan iya ba gskya
Shiru kawai mummy tayi don tasan zafin halin da Ahmad yake ciki ne yasa daddy yake wadannan maganganu
Su fito da niyyan zuwa asibiti maryam ita kuma sun gama magana kenan da nabeel zai wuce
Mummy kanta bataji dadin ganinsu ba sai taga kaman maryam bata damu da halin da dansu yake ciki ba sai kuma ta batsar
Balle daddy da ko kallon su baiyi ba
Bayan nabeel ya gaishe su ya wuce sai maryam tace mummy zan biku asibity
Okay kawai mummy tace
Daddy na jaye da motar mummy na gefe sai maryam a baya
Maryam tace mummy inada magana ppls
Taci gaba da cewa yanzu muka gama magana da nabeel
Sai kuma tayi shiruDuk sun dauka cewa zatayi akan yaushe zaayi auren ne
Daddy har ya shirya ansar bata akan taje kawunta ya daura mata aure
Sai kawai tace mun hakura da juna na bashi hakuri saboda inason in auri yaya Ahmad don ceto rayuwar shi...
Da sauri daddy ya juyo ya kalli maryamMummy ma kallon ta tayi
Sunji dadi sosai daddy sai sanya mata albarka suke
Mummy tace lallai maryam kin cika yar halak. Allah ya saka maki da aljanna kuma ya baki yaya masu maki biyayya kuma ya sa karkiyi dana sanin wannan hukuncin naki
Ta ansa da Ameen
Taji dadi sosai yadda ta sanya su daddy farin ciki
YOU ARE READING
AUREN DOLE sabon Salo
Romancelabari ne me ban tausayi dakuma nuna cewa duk abinda Allah ya tsara ma mutun sai yafaru