AUREN DOLE sabon salo
Part 26
Raqiyya benaMummy ta kalli Ahmad fuska daure tace ka sake ta? A maraice yace no mummy ban sake ta ba
Mummy ta kalli maryam tace yaushe ya sake ki? Maryam ta cire wayarta ta gwada ma mummy message din
Kallon shi tayi fuska daure tace shine don ka raina ni zakazo kana ce min wai wani bai saku ba? Saki ko ya saku tunda har kayi shi yanzu inhar maida maryam zakayi saide in ta amince
Tashi kawai tayi ta wuce maryam tabi bayan ta
Ahmad kuwa zaunawa yayi yana maimaita kalmar innalillahi wa inna ilaihirraji'un
Zuciyar shi sai tafarfasa takeyi
Surar maryam kawai ke dawo masa a rai
Ya san yana ganin hadaddun mata yana muamala dasu amma maryam daban ce
Meyasa bai kula ba sai yanzu?
A cikin zuciyar shi kuwa yayi alkawalin ko ta wane hali sai ya mayar da maryam matar shi
Ya rasa gane son ta ne yakeyi ko shaawar ta?
Mummy ta kalli maryam tace, karki damu maryama kinji? Kina gama idda kika samu mijin ki aure zamuyi maki
Ahmad ba alkhairi bane a gareki tunda kinka ga haka ta faru
Na tabbata maryam insha Allah zakiji dadin rayuwa zuwa gaba zaki samu wanda ke sonki kema kina son shi kiyi auren ki
Mukuma kici gaba da daukar mu iyayen ki
Maryam sam bata san me keyi mata dadi ba, wani son Ahmad ke ziyartar ta a lokacin
Gaba daya kalaman mummy basu ma shigar ta
Yanayin Ahmad kawai take tunawa
A fili kuwa sai tace ma mummy toh nagode mummy Allah ya saka da alkhairi
Ta shiga dakin ta tarufe kofa ta zauna tana tunanin yadda zata fara rayuwar ta a yanzu da batada aure
Tun lokacin da tasan kan ta a kuntace rayuwar ta ta taso
Saurayi daya ta taba yi a rayuwar ta kuma aka raba ta dashi karfi da yaji
Koda aka mata aure kuma ta samu yanci harda zuwa makaranta amma batada freedom na koda magana da saurayi ne saboda tana da aure
Shiru tayi kawai ta koma ta kwanta tana nazarin yadda tayuwar ta ta kasance
A bangaren Ahmad kuma
Tunda ya fita daga falon ya shiga part dinshi inda Aish take da me kula da ita ya rungume ta jikin shi yana faman sauke numfashi sannu sannu
Aish cikin gwalancin ta tace dada ina chokulet ina? Dayake dada take kiran shi
Ya dago jajayen idanun shi ya kalli Aish, mami ya tuna da ita
Mami ce kawai macen da ya zauna da ita tana son shi tsakani da Allah shima yana son ta
Ya tuna safiyya da yaso sosai amma ta walakanta shi sam ko labarin ta bai kara ji ba
Maryam ko chance din zama cikin rayuwar shi bai bata ba fiye da shekara biyar da auren su amma ko maganar minti biyar bai taba yi da ita ba
Yanzu kuma lokaci daya kawai yace ya sake ta
Wata zuciyar tace kuma gashinan ka kamu da son ta..
Yayi saurin karyata zuciyar shi da cewa shaawar ta dai nakeji... bana son ta mami kawai da Aish nakeso..
Kukan Aish ne ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya fada
Ya kalli Aish yace lafiya Aish? Kuka kawa taci gaba da yi
Shi sam bai san tayi ta mai magaba ba baya jin ta saboda ya fada duniyar tunani...
Yace oya sorry baby I'll get you chocolate kinji? Ta dan yi shiru sannan tace i will go with u dada
Haka ya dauki diyar sa ya kama hanyar fita gidan
Suka yi shopping dinsu ya dawo ya aje ta wajen mummy sannan ya tafi zuwa wajen sabuwar budurwar shi zeee zeee wadda suke sheke ayarsu a yanxu
Shin ina su anty saratu
Sun dade suna kashe kudi akan Ahmad ya auri zee zee amma inaa
Sun dai samu sun tura ta yana zaman iskanci da ita don shi sam bai ma san ta hada wani abu da maryam ba....
BINABASA MO ANG
AUREN DOLE sabon Salo
Romancelabari ne me ban tausayi dakuma nuna cewa duk abinda Allah ya tsara ma mutun sai yafaru