kuliya kuliya...

185 7 0
                                    

006... "Kuliya Kuliya cinye min kashina" inji Sahla...

Yau Alhamis tunda na dawo daga school na fara kokarin yin assignment ɗin English da aka bamu dan gobe da safe za a karɓa. Ina son darasin English saboda shine kaɗai ko ban yi karatu ba na kan taɓuka abin kirki.

"Sahala tashi ki karɓo min Abinci tunda ke yunwar bata ishe ki ba"

"Kaka Dan Allah ki bari na karisa rubutun nan"

Can kamar minti ɗaya Kaka ta sake yi min magana. Na shareta.

"Sahala wai sai hanjina sun gama nannaɗewa ne kan za ki kawo min abincin ne"

"Kai Kaka" na dangwalar da littafin na je ɗaya ɗakin na ɗauko cooler na wuce sashin Anty Amarya. Na rike ranan girkin kowacce a cikinsu kamar yadda na rike irgen kwanaki.

Ina nufowa ɗan karamin gate da ya raba ɓangarenmu dana matan gidan na fara jin hayaniya. Muryan Anty Amarya ne ke tashi. Ban taɓa ji tana masifa irin haka ba. Ina zuwa kofarta na tarar da kaya jibge a wajen. Hayaniyar ta ciki ne. Na kutsa kai na shiga.

Fitowa kawai take da kayanta daga ɗaki tana jibgawa a falo. Su Mama da Ummi na wajen suna bata hakuri amma sai masifa take.

"Ni zai nunawa ya san Amana. Ya san sarai inda ya ɗaukoni ba gidan matsiyata bane. Aure shekara goma miya tsinana min. Dan ban haihu ba nina ke hana kaina haihuwan ne. Yau zan bar masa gidan. Bani da kowa a gidan nan amma wani irin bauta ne bana yiwa 'ya'yan gidan"

"Sai hakuri dai Rafee'ah" Mama ta faɗa tana kokarin matsar mata da akwati gefe dan Anty Amaryan ta samu ta ajiye jakar da ta fito da shi.

"Zan bar masa gidansa. Alhamdulillah tunda ba wajen zama na rasa ba"

Shegu sai hakuri su ke bata amma babu wanda yai yunkurin hanata tattare kayanta. In da babu munafurci ai Kaka zasu kira ta zo ta hanata tafiya amma suka makale suna bata hakurin karya.

"Anty Amarya Dan Allah ki yi hakuri"

Allah na gani na fi sonta duk cikin matan gidan nan. Idan ta tafi ya zamu yi ni da Kaka.

"Matsa min a waje kiga" ta ɗan bugeni kaɗan ta wuce da wasu akwatunanta waje.

"Wai ina Hamza ne?"

Mama ta ɗan karkatar da kai wajen Ummi tace " ni kam Akwatunan Rafee'ah nawa ne? Wancan kam ba irin akwatin lefen Firdausi ba"?

"Irinsu ne fa. To yaushe ta sauya akwatuna"

Shigowar Anty Rafee'ah yasa suka yi shiru. Na yi mamaki ma da annamimiyar gidan bata shigo ba, kila bata nan ne.

Na fito daga falon na nufi ɗakinmu. Yadda Anty Amarya ke fitar da kaf kayanta bana tunanin ta yi girki yau.

"Ina abincin? Ko bata gama ba"

Ashe ma na bar kular tamu a chan.

"Kaka, Anty Amarya fa yaji za ta yi. Gata chan tana tattara kayanta"

"Yaji kuma?. Miya faru?"

"Ni ina zan sani"

Kaka ta mike daga tabarmar da take zaune tace mu je. Na bita a baya dan nima ina son sanin abinda ya faru.

Lokacin da muka je Kaninta Hamza ya zo yana ɗaukan mata kaya yana kai mata zuwa motarta. Dama duk gidan ita ke da mota ta kanta, sauran kam sai dai su yi amfani da motan gida na Alhaji.

"Rafee'atu ya haka? Mi ya kawo maganan yaji"

"Hajiya Kaka kiyi hakuri ki tambayi ɗanki"

"Rafee'atu ban san ki da rashin kunya ba. Mu shiga ciki ki gaya min abinda ya faru"

SAHLA a Paris (Hausa novel)Where stories live. Discover now