the plan

199 4 0
                                    

TOP-NOTCH.....the touch of excellence just for you.

✈✈✈SAHLA a Paris✈✈✈

014...The Plan...

Ina zaune ina rubuta review Anty Amarya ta yi sallama.  Kaka na zaune ta yi nisa da tunani.

"Sahla dan Allah ga Ayman nan ki kula min da shi kafin na dawo. Muna da surgery ne ba zan iya tafiya da shi ba. Akwai abincin shi a nan, idan akwai abinda na manta ban saka ba ga key nan ki je ki ɗauka"

Tab. Anty Amarya ce da barin key ɗin ɗakinta. Kai ashe reno na chanja mutum.

Na karɓi Ayman ina mishi wasa. Lokacin da aka kawo shi Alhaji ya tara dukka gidan aka yi meeting yace mana Ayman ɗan Anty Rafee'ah ne dan haka ɗansa ne. Ko bayan ransa bai yafe ba wanda yaiwa Affan kallon ba ɗan Kabiru Ubandoma bane.
I remember har sunan Ummi da Umma Bilki ya kira ya ja musu kunne akan duk wacce ta yiwa Ayman gorin asali a bakin aurenta.  Alhaji yayi faɗa sosai.

A ranan sunansa anyi shagali sosai. Bayan sati biyu da sunan shi Ummi ta haifi 'ya mace. Ta sha burin namiji zata haiho amma Allah ya turo mata 'ya mace.
Tun kafin ayi suna aka fara rikici da ita akan Alhaji ya ki sake hannu ayi shagalin suna kaman yadda aka yiwa Ayman. Rabon da ayi haihuwa a gidan ai an jima. Alhaji yace ba za ayi shagali ba.

Ita dai yarinyar ba a saka mata suna Fatima ba sai aka saka mata Khadijah muna kiranta Baby Dijah...

"Kaka ta yi bacci ne?"

"Ki bar Kaka fa. Kuna magana yanzu zata bige miki da bacci"

Anty Rafee'ah ta fita bayan ta yiwa Ayman kiss a goshin sa.

Yaron kyakykyawa da shi, idan ba a faɗa maka ba baza ka taɓa sanin ba Anty Amarya ta haifeshi ba. Shima fari ne sosai kamarta.

Da na ga yaron zai hanani rubutu sai na ɗaura shi akan gado, ya ɗan yi kuka kaɗan yai shiru ya fara bacci.

Ina rubutu Kaka tace " Sahala yanzu wai Kabiru da AbdulKarimu ba zasu biya mini kujerar Makkah ba. Anya ba zan sai da Tumakai da Awaki na ba?"

Na yi dariya nace " Kaka kenan, kuɗin jirgi fa ba kuɗin motar Gombe zuwa Abuja bane. Kaka kema ki hakura da maganan nan, kwanan nan fa kullum sai kin yi korafin kafanki"

"Kema goya musu baya zaki yi. Ai ina gani a TV masu lalurar kafa na zuwa Hajji, zaka ga ana turasu a keke"

"Kaka idan aka ce za a biya miki kujera ma ni zan ce kar su biya. You are so obssessed..." kwal na ji sanda a kaina.

"Amma Kaka Allah, Allah kina cin zalina, nifa marainiya ce"
Ta ɗaga sanda za ta sake kwaɗamin na yi saurin jan littafina na gudu...

*

Su Abba zasu dawo Nigeria da zama. A bakin Kaka na ji yau dana dawo daga lectures.
Na yi ko oho da labarin. Ni ina ruwana da su, idan ka cire Abba dukkansu ba ruwana da sha'aninsu.

"Ni kam ba zance kuke da Afan ɗinba"

"Allah ya kiyaye na yi zance da shi. Ni fa Kaka ki barni, karatu zan yi mai zurfi sai na ga karshen biro"

"A'a ki zama Alhudahuda karshen karatu kenan. Ke da nake so ki shirya da Yusufa nayiwa Kabiru magana a yi 'yar gida nan da farkon shekara mai zuwa"

"Kaka karatu zan yi. Ba ruwana da aure. Mai ake yi a aure banda cire kunya"

"Auren ne ba amfani. Ita Asiya data sha boko ta koshi gashi har yanzu babu mashinshini. Ina raye ba zaki karisa boko ba sai a ɗakin mijinki. Ba kya ganin Asiya ne"

"Kaka kenan, ke kika ce jifa aka yiwa Anty Asiya yanzu kuma kince boko ya hanata aure. Da aure da mutuwa duk lokaci ne. Ke ya ba ki mutu ba da Inna Sadiyya ta rasu."

SAHLA a Paris (Hausa novel)Where stories live. Discover now