*AMARYAR ZAYYAD*
Na
©®Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabirPage 12.
Rashida da sauri ta ɗauki tsintsiya ta fara sharar falo a lokacin Zayyad ya shigo da sallama, ta amsa tana ɗan sakin murmushi domin mamansu sosai ta yi mata huɗuba fushin da tayi da shi, shiyasa ta ɗauki aniyar sauyawa domin ta sauya salo, tayi masa sannu da zuwa ya amsa tare da yin hanyar kitchen dan ya saka ruwan wanka saboda yasan bata saka masa a flaks ba, yana shiga yaga yadda ya barshi ɗazun haka ya same shi hakan ya tabbatar masa da Rashida bata daɗe da dawowa ba kuma bata gyaran gidan ba kafin ta fita, hakan ya ƙona masa rai amma in da sabo ya saba, dan haka juyawa yayi ya wuce zai fita ta dakatar dashi da sauri.
Ina kuma zaka je? Me zan dafa mana ne.?
Zayyad ya juyo yana dubanta da kyau.
Rashida bana buƙatar komai kuma ki daina yi mini tambayar ina zani tunda ni ba ɗanki bane.
Amma ai naga yanzu ka dawo kuma nice da girki.
Ashe ma kin san ke ce sa girki shine zaki je kiyi zamanki baki dawo da wuri ba, sannan kin fita baki gyara gidanki ba wannan wace irin rayuwa ce.
To ai yanzu zan gama komai In Sha Allah, bari na saka maka ruwan wanka a kettle.
Ki barshi kawai dan kinsan bana son jira, kuma yanzu ba ke kaɗai bace ina da damar da zanje inda zan samu farin ciki. Aslam zo muje ɗakin antynku.
Ya ƙare maganar dasu Aslam, Rashida tayi saurin dakatar dasu.
Ba inda zasu je, Matarka bata son yaranka dan cewa suka yi tayi musu faɗa har tana ce musu ba su da tarbiyya.
Safnar ce zata ce haka me suka yi mata? Ilham me kuka yi mata har tayi muku faɗa.
Wai daga Aslam yaga abinci a center table ya fara ci, sai kuma muka shiga bedroom muka ɗiba cincin, shine wai ba mu da tarbiyya har take mana faɗa meyasa zamu ci bada izininta ba.
Eh mana Abba faɗa tayi mana shine mu kuma muka yi fushi muka bar mata ɗakinta, dama mamanmu tace duk abinda tayi mana in ta dawo mu faɗa mata shine...
To faɗi ba a tambayeka ba, fara rattafo zance rarara kamar wanda ya haɗiyi radio.
Cewar Rashida data katse shi cikin faɗa, Zayyad ya gyara tsayuwa yana ƙara haɗa maganganun yaran a kansa ya tabbatar tunda Aslam ya faɗi haka to Rashida zata aikata.
Kin kyauta kin ji, da kanki kike son ɓata tarbiyyarsu, na tabbatar baki ji ba'asin faɗar data yi musu ba kike niman yanke mata hukunci.
Ato yara da gidan ubansu sannan ta san kana da yara ta aureka dole ne tayi musu uzuri matsayinsu na yara.
To amma tarbiyya ce kice musu duk abinda tayi musu su faɗa miki, wannan ai sakarci ne kina so ki ɗaura raya a turban da bai da kyau, Rashida ban san me yasa kika sauya ba wlh, da farko kin nuna kina tare da Safna amma tunda tazo gidan nan kike ta abu daban daban masu cike da mamaki, ban taɓa zaton haka daga gareki ba, dan haka ki sauya hali in ba haka ba ke ce zaki wahala.
Dama ai komai nayi laifi ne yara ne kuma In Sha Allah ba zasu ƙara zama a gunta ba in yaso sa riƙa jirana a maƙota, itama zata haihu ai zata san zafinsu, tarbiyya dai dai gwargwado ina basu Allah ya sani ai.
Ban da lokacinki, Ilham zamu je gurin antynku ku bata haƙuri.
Ba in da zasu maza ku wuce kuje ɗaki ku cire uniform.
Sum-sum yaran suka wuce Zayyad ya girgiza kai ya fice. Da Safna ta buɗe masa da farararta tace.
Sannu da zuwa farin masoyi yau ka dawo da wuri Allah yasa dai lafiya.

YOU ARE READING
AMARYAR ZAYYAD
General FictionSanin abinda ke cikin labarin sai an bini daki daki amma akwai sarkakiya.