SANADIN MATAR UBA

767 10 0
                                    

SANADIN MATAR UBA





Oum.... Now and old







_Sakamakon qorafi na wasu masu qarancin fahimta yasa dole badon munaso ba zamu mayar da littafin nan na kudi akan farashi daidai aljihun kowa just 100 kawai idan kinaso tuntubi wannan number zaayi Miki bayanin yanda zakici gaba da samunsa cikin sauqi._

_09013718241_






33






A bangaren su Hajiya saratu kuwa sun isa kasa mai tsarki lpy inda kowa yake ibadar sa ba ruwan sa da kowa musamman Ummi da ta maida hankali akan  yi wa iyayen ta addu'a kullum tana masallaci lokaci bayan lokaci suna waya da janniy amma duk yanda janniy taso suyi sex chat Ummi sai ta ki yarda ta nuna mata ta fiso su hadu kawai idan ta tambayeta tana ina taxo sai tace ai yanzu suna tare da alhaji dan dole janniy take hkr







Tsakanin Ummi da Hajiya saratu wata amace mai karfi ta kullu dan yanzu Hajiya saratu ko yaushe suna tare da Ummi idan basa hira to suna masallaci komai tare sukeyi kai hatta abinci ma ita dai Ummi bata kawo kamai a ranta ba amma ita kam Hajiya saratu kullum saita saka abubuwa da dama akan ummi sabida haka ta ke bude mata duk wani sirri nata yanxu Ummi duk wani kasuwancin Hajiya saratu ta sani duk abinda take yi kai hatta kayan da Hajiya saratu ta tura 9ja wannan zuwan Ummi tasan dasu sabida haka sai itama ta saki jiki da Hajiya saratu sosae  ta ma daina mata kallon kishiya baki daya zaman su suke na amana






Hmm su alhaji Sauban kam an nutsu sakamakon anzo gurin nutsuwa shima ba ruwan sa da duk wasu mata duk da ba karamin kokari yake ba abinka da sabo a haka suka samu suka kammala umrar su ana washe gari zasu dawo 9ja nehh Hajiya saratu da Ummi ska shiga kasuwa suka yo siyayya da dama ta tsaraba da kayan ciye ciye kai harma sarin kayan ta na chan duk sunyi sun kammala





Alhaji Sauban yayi waya a gida inda yasa aka sake kayan duk wani vangare na gidan su safna suna ganin an fara gyaran gidan su ka San alhaji nehh zai dawo dan haka hankalin safna yayi bala'in tashi gashi jikin ta bai gama warkewa ba kenan mai zata cewa hajiyar ta jamsy ce ke tausar ta tana nuna mata ba komai karta damu insha Allah zata San yarda zata bullowa matsalan






Safna kam kallon ta Kawai tayi dan tasan ba abinda zata iya kawai tana fada nehh dan hankalin ta ya kwanta amma sai tace to mai ya kamata muyi kenan dan ganin basu gane da hakan ba






Jamsy tace ni dabara guda daya nehh kawai idan sun dawo Mu nuna mun gaji da zaman nan gidan saimu koma gidan Mu ina ganin hakan zaifi bayan kin warke sai ki dawo






Kai kawai safna ta kada amma ba dan ta yarda wannan shawaran zai bulle dasu ba



Washe gari jirgin su alhaji Sauban da Hajiya Ummi da Hajiya saratu ya sauka a gida Nigeria a filin jirgin Malam aminu Kano





Tun kafin su sauka driver yaje dukar su dan haka suna sauka kawai gida suka taho kai tsaye





Alhaji kam ana isowa ban garensa ya nufa ba tare da ya kula ko daya daga cikin su ba




Ganin haka nehh yasa haj Ummi yin turus da mamaki a fuskar ta Dan ba haka ta zata ba ta zata zata sauka a cikin sabon gidan ta Kawai dai sai ta kanne ta wuce bangaren ta Kawai bata kula haj saratu ba







Ita haj saratu nata bangaren ta wuce inda ta samu komai fess kamar yarda tayi tunani dan haka dakin ta Kawai ta huce ta fada ban daki wanka tayi ta fito ta Sa kana nun kaya ta kwanta dan huce gajiya ba jima wa bacci ya dauke ta Sam tama manta da batun wata yarta safna ikon allah🤔







SANADIN MATAR UBAWhere stories live. Discover now