SANADIN MATAR UBA

1K 9 1
                                    

SANADIN MATAR UBA



Oum.... Now and old


_Sakamakon qorafi na wasu masu qarancin fahimta yasa dole badon munaso ba zamu mayar da littafin nan na kudi akan farashi daidai aljihun kowa just 100 kawai idan kinaso tuntubi wannan number zaayi Miki bayanin yanda zakici gaba da samunsa cikin sauqi._

_09013718241_


21







               AFTER 1 MONTH


A wannan lokacin an sallami su kalid daga asibiti Dan duk sun warke ma na laifi Dan kalid har taka kafar Sa yakeyi Dan haka ba karamin dadi iyayen sukaji ba kusan koh da yaushe kalid da imran suna tare basu da wani lbr saina su safna da jamsy Dan haka abin ya fada damun iyayen nasu baki daya sabida haka sai iyayen suka yanke shawarar samun yaran nasu idan aure nehh sai ayi musu da yaran Dan maganar yaran zata iya zautar dasu baki daya





Suko su safna SANDA aka sallamo su daga asibiti ba a bari sun hadu dasu kalid ba kwata kwata Dan minister amjad nehh ya hana hakan Dan yace hakan zai daga musu hankalin yara Dan haka driver kawai aka basu har kofar gidan su safna aka sauke su driver din yayi tafiyan sa






Tsayawa safna tayi tana kallon kofar gidan Dan tsoron shiga takeji ace wata daya baya gida to ina taje sai a wannan lokacin tayi Dana sanin su imran a rayuwar ta wani hawayen takaici nehh ya zubo mata jamsy ce ta fara lallashin ta tana bata baki



Safna da gaba daya tazo wuya da kyar take magana tana fadin safna ki duba fahh ki gani wata daya bama gida to ina mukaje ba mamaki su mom dinki sunzo dubamu bama nan kinga muna cikin tsaka mai wuya tun da bamusan koh sau nawa sukazo Neman Mu ba kuma yanzu haka ma idan mun shiga mai gadi sai ya tambayeni Inda mukaje shima muce masa nehh Dan ma Allah yasa ba wani tabon ciwo a jikin mu ko daya da ba mu da bakin mgn








Jamsy tace ki kwantar da hankalin ki indai wannan matsalan nehh ni zanji dashi kinji bestyna yanzu xo muje mu fara gamawa da baba






Ba tare da tsoron komai ba suka shiga gidan dan safna ta yarda da jamsy din ta sabida haka ta cire tsoro baba mai gadi na ganin su ya taho da sauri yana zuwa ya tsuguna a gaban safna yana fadin uwar gidana ta kaina ina gwanin wani ga tawa ni nasan kinaji dani ta gaban goshin alhajin mu ina akaje kwana biyu haka naga bana ganin ki yau kusan wata guda kenan




Kakalo murmushi safna tayi tare da kallon jamsy kada mata kai jamsy tayi sannan ta kalli baba mai gadi tace baba munje kauyen su jamsy nehh sai yau muka dawo mun manta bamu fada maka bane ko anzo Neman mu nehh





Baba mai gadi yace ehhh tabbas anxo Neman Ku sosae ma kuwa




Dammmm gabansu ya fadi jamsy tace suwaye sukazo Neman mu baba




Yace ai ba wasu na waje bane iyayen Ku nehh na wajen ki ya nuna jamsy yace sunxo ya kai sau biyar amma ina ce musu kunje wani biki nehh wata rana nace dinner har fada sukeyi suna cewa dama abinda aka turoki Ku taru kuyi a gidan kenan haka dai suke tafiya amma yau basu zo ba gsky Dan dama wannan satin suka fara xuwa







Wani sanyi jamsy da safna suka Ji a ransu tabbas Allah ya taimkesu d baba mai gadi ya yi wannan karyan



Murmushi safna tayi kafin tace gsky mun gode baba ba abin da zamu ce ma sai gdy





Yace ai ba komai YAR nan amma nan gaba Ku rika sanar da wani irin wannan tafiyar sabida gudun matsala


A tare suka furta insha Allah sukayi cikin gidan cikin tsananin murna Mara misaltura





SANADIN MATAR UBAWhere stories live. Discover now