SHAFI NA ƊAYA

257 10 4
                                    

*MAI SAƘO*
   *(GARIN NEMAN GIRA..)*

*BILKISU GALADANCHI*

*ADABI WRITER'S ASSOCIATION.*

 Arewa books at: https://arewabooks.com/book?id=6646536dc575fcfa9ee217d8

*Da sunan Allah mai rahama mai jinƙai, yanda Allah ya bani ikon fara wannan rubutun ina roƙon Allah ya bani ikon ƙarasawa cikin aminci ya kuma bani ikon rubuta alkhairi duk wani ɓatanci da sharri Allah ka haneni da rubutawa Ameen.*

  01.

Kamar 'yar kaza haka ta ɗakkota gaba ɗaya daga jikinta har na yarinyar jinine sosai,  farar rigar likitocin da ke jikinta ta zama ja, a ƙarƙashin rigar kuwa doguwar rigar atamfar jikinta mai adon ja da milk colour ta fita hayyacinta gaba ɗaya tabarau na idonta a karkace yake bayan haka garin koƙarin gyaranshi da ta ke ya haddasa masa sauya launi zuwa jajaja har bata ganin gabanta a ido ɗayan da ya stain.. Tana isa wurin Mijinta ta zube 'yar a hannunsa sannan ta ce "Na shiga uku Dr. Wallahi jinin yaƙi tsayawa nayi packing ma amma yaƙi na rasa yanda zanyi." Bai gama saurarar me za ta ce ba ya juya da sauri har yana haɗawa da gudu zuwa ɗakin duba mara lafiya jikinsa har na rawa shi ɗinma ya shafe 30mns yana ƙoƙarin ganin ya tsayar da jinin da ya ɓalle kamar da bakin ƙwarya amma abin ya gagaresa, duk Ac da fan da ke ɗakin suna aiki bai hanasa haɗa wani uban gumi ba mai tashin hankali, a hankali ya soma ja baya yana kallon yanda idon ta ke lumshewa lokaci ɗaya ƙirjinsa yana ƙara bugawa,zuciyarsa kamar zata faso ƙirjinsa ta fito, kallon ƙofar ɗakin ya yi ya zubewa Dr. Rash ido dake kallonso ta glass da ke jikin ƙofar ɗakin hawaye na sauka akan idon ta a hankali. Takowa ya yi ya buɗe ƙofar kafin ya ce

"Call your team Rash there is nothing we can do ourselves kafin lokaci ya ƙure mana." Hannunsa ta riƙo a rikice "Haba Dr. Try and do something don Allah this is your field don Allah save our only daughter." Lumshe idonsa ya yi ya buɗe cikin tashin hankali zufar har saman hancinsa ta ke tsiyaya idon nan ya kaɗa ya yi jajir da ƙyar ya iya furta kalmar "Rash Please do as i say call your team immediately she is loosing too much blood and i am loosing hope na kasa komai." Runtse ido Dr. Rash ta yi cikin jin zafi da wani kalan raɗaɗi kafin a hankali ta ce

"Wannan yana nufin tonuwar asirina Dr. Malik, wannan yana nufin rugujewar farin cikina kasan yanda na tsani abortion da masu yi, kasan yanda muke hanawa ayi irin wannan a asibitinnan yaya zan ɗauki wuƙa in daɓawa cikina????" Cikin hargowa ya ce "To hell with your so call rules call your team immediately." Wani irin kuka ne ya duɓuce mata jikinta yana rawa ta zaro wayarta a aljihunta ta kira Dr. Fati tana ɗauka ta ce

"Dr. Fati Please idan kina kusa kizo MVA room da ke sama my meenal is dying, call Dr. Ashraf and Oga Milton." Daga haka ta katse wayar within 10mns suka iso kai tsaye suka duƙufa kanta Dr. Fati ta kalli Dr. Rash ta ce "What happen to her?"  A raunane Dr. Rash ta ce "Please just try your best and save her na kasa komai she is loosing too much blood and i am scared of loosing her." Oga Milton ya kalli Dr. Ashraf yace "Tasha magaungunan zubar da ciki kuma beyi ba anzo anyi MVA kuma an tarwatsa mahaifar look how her tommy is just getting bigger kamar zai tarwatse i suggest emergency theatre now arrange our team immediately we have to remove the placenta." Ragwaf Dr. Rash ta zube jin zantutukan Oga Milton yayinda Dr. Malik ya dafa bango jin jiri yana ɗebarsa kafin a hankali ya sulale ƙasa shima, har aka wuce da ita Theather ba wanda yake ƙwaƙwaran motsi a cikinsu.....
  After 4hours.

Kai tsaye ICU aka wuce da ita hankalin dukkan likitocin ya tashi saboda har bayan cire mahaifar jini take zubarwa kamar ba gobe, jinin yaki tsayawa sannan da ƙyar ta farfaɗo shima ba wanda take ganewa, har washe garin ranar bata farfaɗo ba sanin cewar she is the only female child a wurin iyayenta kuma she is just 15 ya sanya gaba ɗaya likitocin suka kasa tunkararsu da jin ba'asi, bayan haka mahaifin yarinyar ke da babbar asibitin da ake ji da ita a garin kaduna. Koda ta buɗe ido ba kowa a ICU ɗin daga ita sai injinan dake taimaka mata wurin numfashi, hannu takai ta janye oxygen da aka saka mata tabi ɗakin da kallo kusan mintuna goma sai ga Dr.Rash ta shigo tare da Dr. Malik binsu ta yi da ido har suka ƙaraso suna mamakin yaushe ta tashi hawaye fal idon Mahaifiyar ta ce "Meenal am glad you are back, Ubangiji Allah ya baki lafiya." Batace komai ba sai binsu da ta ke da ido mahaifiyarta ta riƙo hannunta tana mata kallon so da murnar ganin ta farfaɗo, a hankali cikin dashashiyar muryar da duk wanda ya ji yasan me muryar na cikin tsananin ciwo ta ce "Mom don Allah idan na mutu kimun addu'a Allah ya yafemun zunubin da na aikata, a islamiyya ma malam ya ce duk macen da ta yi zina harta mutu bata tubaba wuta ake sakata, kuma ya ce duk masu zubar da ciki sai Allah ya kamasu amma Momy nace karki zubar ai ko? Ance gwara zunubi ɗaya yanzu ni da zan mutu idan na tafi kenan wuta za'a sakani, Allah na tuba astagfirullah ya rahman Allah ka gafartamun." Cikin kuka Mom ta ce "Noo My Baby ba za ki mutuba in shaa Allah, kuma ki tuba tsakaninki da Allah akan ba za ki sake aikata zunubinba har abada sai kiga Allah ya yafe miki shi mai gafara ne kinji." Murmushi yarinyar ta yi kafin ta ce "Allah na tuba astagfirullah,. Astagfirullah wa atubu ilaik in shaa Allah bazan ƙara ba, amma momy Ya Zuhair fa?" Shiru momyn ta yi bata amsa ta ba a hankali yarinyar ta ce "Mom Please ku yafe masa kunji, nima ku yafemun and i really want to see him again don Allah ku kiramun shi." Shiru Mom ta yi sai Dad ne ya ce "Zanje in taho miki da shi yanzu kinji Dadys pet." Daga haka ya juya ita kuwa ta lumshe ido tanajin gaba ɗaya kamar tana shillo ne tsabar yanda gaba ɗaya take jin jikinta kamar ba nata ba kwata kwata ji take kamar kaine kawai a jikinta don sakwai take jinta kamar ƙashi da rai... Sunanan shiru har zuwa sanda Zuhair da Dad suka iso ɗakin. Zuhair ya tsaye daga nesa kaɗan yana kallonta lokaci guda hawaye suka cike idon sa ya rasa me ke masa daɗi ganin his only sister lying on bed kamar ba ita ba gaba ɗaya har leɓenta ya yi fari kamar gawa ga ƙarin jini ana mata jinin da ke zubewa ana sakawa yana zubewa yanda aka saka, hannunta ta ɗaga da ƙyar ta miƙa masa ya tako a hankali ya kama hannun nata cikin tsananin rauni trying his very best not to cry, a hankali ya ce

"Ki yafemun Lil sis kinji don Allah ki gafartamun na gama lalata miki duniyarki ina zan saka kaina inga Haske." Ya ƙarashe maganar yana kukar fitan hankali." Murmushinta mai kyau ta sakar masa kafin ta ce

"Ya Zuhair kuka baya maka kyau now remove that crying face and put a smile on your face i want to die watching you smiling, baka taɓamun komai ba kaji, su mom ma nace su yafe maka we did that awful and shameful act together we never wish for that to happened haka nima, ba tarbiyan su momy bane amma suyi haƙuri." Shiru duk ɗakin aka yi sai sautin kukan Zuhair a hankali Dad ma sai ɗauke hawayensa ya ke in style yayin da mom ma kukan ta ke amma mara sauti a ɗan tsame Meenal ta ce

"Na san ina mutuwa yanzu wuta zan shiga, because of what i did my Dad, my mom and my caring brother are crying tayaya Allah zai yafe min, malaminmu na islamiyya ya ce duk wanda ya mutu da fushin iyayensa akan sa bazai taɓa shiga aljanna ba ba zai samu rahamar ubangiji ba, ni kuma duk na gama ɓatawa Family na rai i ruined my family don Allah kuyi hakuri ku daina kuka, i really regret everything na tsani kaina i can't stand this anymore." Ta fashe da kuka, nan da nan Zuhair ya ƙara ruɗewa ya matsa kusa da ita ya riko hannunga duka biyu

"Noo Please don't say that My cute little sister, ba wanda ya ke fushi da shi right mom right Dad?" Ya ƙarashe maganar yana kallonsu cikin ido nan take suka soma gyaɗa masa kai tabbacin hakane, "we all are crying because we are happy the operation was successful and you will be fine again kinji, nobody is angry with you." Murmushi ta yi kafin ta ce

"Yaa Zuhair you know that well we promise to buld together Allah ya bamu ladansa, promise you will it for me ko bayan na mutu and remember you promise to buy my first uniform idan na shiga nursing school karka mata ance likkafani fari ne use your own money and buy it for me idan na mutu, kuma karka manta munce zamu buɗa islamiyya idan muka girma muka samu kuɗi to ka buɗa last last ranar da mukaga mahaukaciya an mata fyaɗe we made a promise to ourselves that zamu buɗe physiatrick hospital free tunda government basa son kwashe mahaukata akan titi you makesure ka cika wannan promise since i will not be able to witness that kaji." Da tausayin kansa ya ce

"Meenal zafin ciwo yana sakaki sambatu shot it kina jina." Murmushi ta yi

"Na ji sauƙi fa, kawai ina maganar idan na tafi abuna ne." Shiru ya yi yana kallonta jikinsa duk ya gama mutuwa ta ko ina. Kallon Mom ta yi da murmushi a fuskarta

"Mom." Mahaifiyar ta ɗago ta kalleta tana murmushin ƙarfin hali Meenal ta ce "Mom Please forgive me kinji, da Dad me Daddy please ku daina fushi da mu ku yafe mana don Allah, wallahi ba za mu ƙara ba ko don saboda haramcinsa ga addininmu kunji." Jinjina mata kai Mom ta yi kafin ta ce "Na yafe miki duniya da lahira Meenal ubangiji Allah ya tashi kafaɗunki." Dad ma ya ce

"Na yafewa dukkanku ubangiji Allah ya shiryar da sauran zuri'ar musulmi da ku baki ɗaya." Tana hawaye ta ce "Na gode ubangiji Allah ya yafe mana kuma." Daga haka ta lumshe ido sun kusa awa guda bata sake buɗe idon ta ba har suka fita suka bar Maheer nan. Kusan awa ɗaya injinan jikinta suka fara ƙara da sauri ya kalli wurin allon computer hankali a tashe ya fita neman likita, shaƙuwa ta fara da wani irin tari sai kuma jini a hanci da baki ko da suka zo da likitocin ta gama sandarewa, mutuwar tsaye Zuhair ya yi jin abin da suke cewa lokaci ɗaya ya zube a wurin a some....

Free pages...

Mom Nu'aiym.

MAI SAƘO (DAGA NEMAN GIRA)Where stories live. Discover now