BABI NA ASHIRIN DA BIYU

11.1K 623 157
                                    


 BABI NA ASHIRIN DA BIYU

Ops! Esta imagem não segue nossas diretrizes de conteúdo. Para continuar a publicação, tente removê-la ou carregar outra.

BABI NA ASHIRIN DA BIYU

Sagir ya tafi ofis, Aisha da Aneesa suka je suka dauki kayanta, ta hada kayanta sosai a babban akwati ta kwashi takardun da zata bukata. Sannan sukayi gaba, Sagir kuwa tun safe ya rasa me daya yake masa dadi.

Komawarta da kwana biyu Sagir ya je makaratarsu, yayi magana da principal a kan Aneesa kasancewar hukumar makarantar sUn san da aurenta, gashi tana fama da laulayi hakan ya sa yace zata bar zuwa har sai lokacin jarabawa ya karato tazo ta zana.

Lesson teacher ya sama mata, tana zuwa har main house suyi karatu.

Hajiya da kanta ta sa Aneesa a mota suka wuce asibiti ta mata booking antenatal. Aneesa ba abun da yafi mata haka kwanciyar hankali.

Washegarin randa suka dawo daga asibiti ne Sagir ya shiga dakin Hajiya, nan ya sameta tana kwance tana jin shigowar Sagir dakin amma tayi kaman tayi bacci don haka ya kyaleta.

Kullum Sagir sai yazo gidan da dare a nan yake hira sannan ya koma gida amma ko fuska baya samu a wurin Hajiya bare ya samu ganin Aneesa, kullum suna manne bare ya samu ya mata magana. An dauki sati a haka, wannan yasa Sagir ya samu Abba.

"Abba daman maganar Aneesa ne, tunda na ga ta dan samu karfin jikinta batun komawarta gida" Duk sabon shi da sakewarsa da Abba ta maza kawai yayi ya yi magana.

Abba yayi kamar bai fahimce shi ba "Ah, har sun gama jarabawar ne?"

Sagir yayi tunanin daman wai suna shirin rike masa mata har sai tayi jarabawa ne?

"Abba jarrabawa kuma?"

"Ka san a wannan yanayin nata tana bukatar hutu sannan ga karatu a gabanta, duk da akwai mai tayata aiki idan ta koma ina ga stress zai mata yawa, saboda haka inaga ka dan kara barinta a nan ta kara hutawa."

Cikin jin nauyi Sagir yace "To shi kenan Abba."

Ya kula kaman wani hadin baki sukayi masa ga uwa uba kwata-kwata wayar Aneesa a kashe ya rasa me yake masa dadi.

Ranar ya gaisa da Hajiya a daki fitowarsa falonta ya samu Aneesa ita kadai ce a nan tana karatu don haka yayi tunanin amfani da wannan damar don ya mata magana, amma cikin ikon Allah ya zauna kenan sai Hajiya ta sa baki ta kira Aneesa wai ta tayata sa kaya a wardrobe, ran Sagir ya baci ita da tazo hutawa bata da lafiya kuma wani aiki kuma za a sakata, sannan mutum da matarsa an haramta musu ko da magana ne bare su kebe. Haka ya mike ya bar gidan jiki ba kwari.

Randa Aneesa ta cika sati biyu a main house ne Sagir ya yanke abun yi don ya kula idan ba ya dau mataki ba abubuwan sa gaba daya zasu daina ci gaba, don yanzu haka ma ya daga tafiya zuwa kasashe biyu saboda rashin sanin madafa.

Aneesa ta gama hira da su Aisha da Hajiya ranar Kamaal ma yana gida sai wajen karfe goma tace musu sai da safe.

Shigarta bangarenta taji mamaki kasancewar a kashe ta bar wutan cikin daki gashi kuma ta same shi a kunne. Don haka sai ta bari akan ta manta ne bata kashe ba ta fita. Ta nufi jikin wardrobe don daukar kayan baccinta ne sukayi ido hudu dashi, da sauri taja da baya tsabar tsoron da taji.

Al'amarin ZucciOnde histórias criam vida. Descubra agora