BABI NA BIYAR
Gaba daya gidan ya hautsine sai kace yau take sallah, banda murna da farin ciki ba abun da ke tashi a gidan Malam Habu na Kunuwal. Yau ga Uwani ta zo daga birni kowa sai cicirondon zuwa ganinta yakeyi, wasu an ce musu Uwani ta dawo tamkar balarabiya don kyau, wasu ko ce musu akayi sai sunje su ga yanda fatarta take sheki kamar an canza mata fata. Ko ma dai menene Uwani dai uwanin da suka sani ne 'yar Inna da malam Habu, wayewace kawai ta kawo wannan canjin.
Yana zaune a kan tabarmar gindin bishiya, inda suke taruwa su rakashe suna hirar banza da wofi, wani sa'in a kawo maganar gidan makwabtansu wani sa'in na gidajensu, a nan ne aka fasa kanun labaran.
"Ai Nata'ala, na gaya maka sai ka ga yanda ta dawo wanke hannu ka taba, ni wani kalan yadin da na hango a jikinta alqur'an ban taba ko mafarkinsa ba. Kai kaga wata dalleliyar motar da ta dawo da ita? tafi wacce ta dauke ta a kyau da girma da komai
Iro yace "Ai ba zancen sanyi, kawai abun da za ayi gobe ka shirya da farin safiya, ka cafko kajin ka guda uku kaje kayi barka da sallah ko za ayi dace"
Nata'ala ya hakimce duk yana jin jawabin abokan nasa, yayinda shi ya gama nisa a tasa duniyar...
Bayan ribibi ya lafa ne suna zaune ita da Inna a tsakar gida Aneesa ta dubi Inna tace "Inna Daddy, ya miki bayanin komai ko?"
Inna ta tabe baki tare da gyara bakin zanin ta sannan tace "Uwani kenan, ai ni magana ta fatar baki ta dade bata hadani da mahaifinki ba, bare kuma abun da ya shafe ki. Ko tafiyar kin nan ma da Malam aka gama komai kafin na amsa."
Aneesa ta gyara zamanta tace "Inna don Allah ina son na san takamammen laifin da Daddy yayi miki, ko kuma abun da ya raba ki dashi. Don ni kam zuwana naje da tsanarsa sosai a raina amma na tarar da shi ba a yanda na dauke shi ba. Na san mun muzanta an zarge ki kuma ta dalilinsa amma don Allah ina son ki fada min."
"Zan fada miki a lokacin da ya dace, yanzu ki fada min, shin kin amince da zabin da ya miki?"
Kan Aneesa a kasa, wannan wani abu ne da take dadewa wajen kashe lokaci don ta samo amsar shi amma a kullum sai ta gano cewa bata sani ba, amma kuma meye amfanin sanin ma?
"Inna don Allah ki fada min?" Aneesa ta shagwabe fuska amma sam Innar ta taki, don haka suka shiga hirar shirye-shiryen sallah. Aneesa ta ja bakinta tayi shiru da niyyar washegari idan taje ganin jinjirar Mairo zata tambayi Mama kuma tasan a can kam za a bata labari.
Da wannan zumudin a ranta tayi bacci.
****** *********
"Yanzu haka zaki fita da sassafe?"
"Inna yanzu zanje na dawo, hala kuma daga gidan Mama ta can zan wuce gidan Falmata."
"Idan kin gama sai ki zo ki sa min hannu a miyar sallar ko?"
"To Inna." cikin dauki ta fice daga gidan. sauri take a hanyarta, duk da kowa ta gani yana son gaisawa da ita a hanya, sabanin da, da kowa yake gudun a ganshi tare da ita.
"Ai ke kam yarinyar nan a gaishe ki da iya doka sammako."
"Mama kar kice min bacci kikeyi, sai kika tuna min da Abuja, sai ki ga mata har taran safe bata tashi a bacci ba."
"wai wai wai, ina ni ina kai tara a kwance, ai sai jiki yayi ciwo. Mun ga tsaraba jiya kaca-kaca, Malam Sule ya shigo har nan muka gaisa ya ajiye mana. Allah ya amfana."
Muryar Baba sukaji ya shigo cikin gidan "a'a baba yau bakaje kasuwar bane?" Aneesa ta fada.
Ya zauna kan kujerar sa mai kwanceccen baya "Bayan an sake ni anyi sabon miji kuma ina naga ta walwala bare zuwa kasuwa?"
![](https://img.wattpad.com/cover/74226191-288-k101158.jpg)
STAI LEGGENDO
Al'amarin Zucci
Storie d'amore#13 in romance hot list. 25/1/2017 Still faring high after months of completion. Thank you. A duniyar Aneesa babu abinda ya kai mata Innarta muhimmanci, gashi Innarta ta tura ta birni ta zauna da mutumin da bata taba haduwa dashi ba iya rayuwarta...