BABI NA SHA HUDU

551 43 0
                                        


       'YA'YAN MIJI‍

Na Umm Asghar

             14
Babu bata lokaci Hajiya ta nemi Baban Aisha da maganar auren da take son kullawa tsakanin Daddy da Aisha inda anan take ya amince da shawarar Hajiya don dama zaman Aisha a haka babu aure ba dadi yakeyi mishi ba.

Ba wani dogon lokaci aka yanke wa auren ba, sati uku kawai aka saka zai kama bayan anyi arbain din Mami da sati daya kenan. Za'a daura auren acan gaya sai a dauko amarya daga can.

Ita kam Aisha bata san wainar da ake toyawa ba har sai da ya rage saura kwanaki goma daurin auren sannan Hajiya ta sanar da ita.

A razane ta dago ta kalli Hajiya da kwata-kwata bata lura da halin da takevciki ba ta cigaba da yi mata nasiha akan hakuri da karbar kaddara aduk yanda tazi mata.

Sai dai sam Aisha bata san me take cemata ba don gaba daya kwakwalwarta daina aiki tayi na wucin gadi, bata san cewar hawaye takeyi ba sai da taji Hajiya ta tabata sannan taji danshin hawayen a fuskarta.

"Kuka kikeyi Aisha, bakiyi na'am da maganata bane yasa kike kuka? Idan kina ganin akwai damuwa sai a fasa don bazanso inyi abinda zan cutar dake ba domin kuwa ke din amana ce a wurina. Ni dama nayi sha'awar kasancewarki madadin Maminku ne saboda kyawawan halayenki da nagartarki zanso ace kin kasance tare da Jafaru ki zame mishi mace ta gari uwa ga 'ya'yanshi don nasan ke kadai zai aura da 'ya'yanshi bazasuyi maraicin uwa ba".

Cikin sheshekar kuka tace "kiyi hakuri Hajiya bawai ina kuka don banyi na'am da maganarki bane sai  don ina ganin idan akayi haka tamkar naci amanar Mami ne data rike ni da zuciya daya tamkar 'yar data haifa, tsawon zaman da ita bata taba bambantani da yaranta ba.

Amma ya za'ayi na kasa bin umurninki bayan dukkan abin da kikayi mini a rayuwata komai zan zama a rayuwa kece sila ya kuwa za'ayi na kasa yin abinda kikeso.

In Sha Allahu zaki sameni mai yin biyayya ga dukkan umurninki matsawar bai sabawa Allah b, Allah ya tabbatar mana da abinda yafi alkahiri".

Sosai farinciki ya lullube Hajiya cewa takeyi "nagode Aisha In Sha Allahu alkhairi na tattare da rayuwarki, Allah yayi miki albarka ya azurtaki da zuri'a ta gari".

Har lokacin shocj bai saketa ba abin daure mata kai yakeyi yadda Hajiya tayi yunanin hada wannan auren sai dai bata bari Hajiya ta gane tana cikin damuwa ba tayi kokarin ganin ta saki fuskarta, sai dai bata iya cigaba da zama a dakin ba sallama tayiwa Hajiya ta koma dakinsu.

Tana shiga dakin toilet ta wuce ta rufe kanta a ciki ta fashe da kukan tausayin kanta. Ita kuma tata kaddarar kenan ta auren mutimin da yayi 'ya da ita. Ta jima cikin bandakin sai da taji ana knocking sannan ta wanke fuskarta ta bude kofar ta fita.

Farida ce a tsaye a bakin kofar. Tsaki ta mata sannan tace "wani sabon salo ne wannan ki shige bandaki ki rufe kinaji ana knocking kinyi banza da mutane".

Ko kallon Farida batayi ba ta wuce ta hau kan gado ta kwanta. Tunda taji maganar aurenta da Daddy ta koma wata sukuku da ita gaba daya ta rasa walwalarta. Kullum Ummie cikin tambayarta abin da ke damunta take amma amsa daya take bata itace babu komai.

Yaya Khalifa ma saida ya kirata yayi mata nasiha akan rashin walwalarta don a tunaninshi mutuwar Mami ce har lokacin ke nukurkusarta sai kawai ta bishi akan haka dinne.

Bata san a wurin wa su Ummie sukaji maganar ba a lokacin saura kwana shida durin auren. Farida da Ummie ne suka shiga dakin suka sameta tana shirya musu kaya a cikin wardrobe. Ummie ce tace mata "Aisha wacce magana naji anayi a cikin gidannan akanki da Daddy?"

Gabanta ne taji ya fadi jin maganar data fito daga bakin Ummie. Daurewa tayi ta amsa mata da "wacce magana kenan kikaji". Wani wulakantaccen kallo tayi mata sannan tace "kina nufin kice bakida masaniya akan batun aurenki da Daddy". Shiru Aisha tayi don bata san amsar da zata bata ba.

Shirun da Ummie taji tayi mata ne ya bata tabbacin cewa maganar da taji ba karya bace kenan da gaske ne Daddynsu Aisha zai aura, wannan wane irin cin amana ne Aisha tayi musu ta rasa mijin aure sai mahaifinsu.

Shi yasa dai mutane ba abin yarda bane, da uta ce maijin haushin yanda Farida ke treating dinta ashe dai akwai abin da Farida ta hango da yasa ta kasa yarda da ita.

Zamewa Ummie tayi ta zauna a kasa don ji tayi kafafunta baza su iya daukarta ba jikinta gaba daya rawa yakeyi.

"Mtsew... ni dama na dade da danin crwa wannan mai kama da bararon zamanta a gidannan ba alkhairi bane, kune dama kuka daukaketa kuka maidata wata tsiya. Na kuma tabbata ita tayi kulle-kullen da har Hajiya tayi tunanin hada aure tsakaninta da Daddy. To wallahi tun wuri kije ki kwance kullin da kikayi wa Hajiya don bazamu taba aminta dake a matsayin matar Daddynmu ba".

Haka suka saka Aisha gaba sunata yarfa mata rashin mutunci amma har sukayi suka gama bata daga kai ta kallesu ba. Ta sani cewa dolene ta aro hakuru ta kara akan nata don wulakancin da zata gani a wurinsu ba kadan bane.

Ko kadan kuma abin da sukayi mata bai bata mata rai ba don tasan dolene suji babu dadi akan sabon matsayinta a wurinsu itama ba dadin take ji ba don dai babu yadda zata yi ne to amma ya kamata su fahimci cewar itama ba yin kanta bane kuma komai yana tafiya ne akan kaddararshi.

Idan har Allah ya kaddara mata auren Daddy bata da yanda zatayi ta guje mishi hakanan idan har babu shi a cikin kaddararta babu abin da zaisa aurensu ya kasance.

Tun daga wannan ranar Aisha ta koma mujiya a cikin yaran gidan. Ko bi ta inda suke batayi don hatta da  Yaya Khalifa da Mu'azzam sun daina amsa gaisuwarta. Ruqaiya da Zainab ne kawai basu canja mata ba watakila kuma don su din yara ne basu fahimci me ke faruwa ba.

Ana saura kwana biyu daurin auren ne Hajiya tace ta shirya Mallam Adamu ya kaita gida. Duk da ba taron biki zasuyi ba anan amma tasan acan 'yanuwanta baza su kasa yin yinin biki ba.

Bata debi wasu kaya ba sai kayan data ware zata bayar. Koda tayiwa su Ummie sallama ba wacce ta kalleta a cikinsu.

Ta iske gidansu a cike da mutane, su kam hidimar biki sosai sukeyi. Tana shuga aka fara mata guda ana ga amaryara ta iso. Ita dai yake kawai takeyi.

Dakin Goggo ta shiga gaba daya jikinta yayi sanyi. Sai yanzu data ga mutane a gidan ta kara yarda bikinta akeyi. Har ga Allah baso aurennan takeyi ba to amma bata da yanda zatayi, bazata iya cewa Hajiya bata son danta ba bayan dukkan abinda ta mata ga kuma Babanta da bayada wani buri bayaga na ganin aurenta.

An daura auren Ja'afara Bello Danmaliki wato Daddy da Aisha ranara asabar da misalin karfe biyu da rabi anan kofar gidansu dake garin gaya. A bangaren ango dai ba wasu mutane bane da yawa suka halarta don bazasu wuc mutum goma ba har shi angon.

An shirya nr akan cewa da an gama daurin aure za'a wuce da amarya. Mutum biyu ne aka shirya zasu raka Aisha gidanta duba da yanayin da bikin yazo musu.

Sosai Babanta yayi mata nasiha ya nuna mata cewa kyakkyawan halinta da nagartarya ne suka saka Hajiya yin sha'awar hadata aure da danta don haka yana so ta cigaba da portraying kyakkyawar dabi'arta ta rike yaran mijinta da amana.

An fito da ita tana kuka sosai don har yanzu ta kasa yardarwa kanta wai itace aka daurawa aure da Daddy. An sakata a motar da dama don tafiya da ita aka zo tare da 'yan rakiyarta.

Sun shiga gidan ana kiran sallar magriba. Ita dai banda faduwa babu abinda gabanta keyi. Tana lullube a cikin mayafi aka shiga da ita cikin gidan.

Gidan shiru babu kowa sai Hajiya da suka tarar a parlour. Ita tayi musu jagora zuwa dakin Aisha dake a sama. Bayan fitarta ne su Yaya Huwaila da Yakumbo Dije ( kanwar Babanta) da suka kasance 'yan rakiyarta suka fara haramar yin sallah.

Yakumbo Dijevce tacewa Aisha ta tashi tayi sallah. Sai a lokacin Aisha ta bude idonta, dakin tabi da kallo. Dakin da Mami take saukar bakinta ne sai dai an canja kayan ciki. Gado ne da wardrobe da madubi kirar italy.

Dama Babanta ya fada mata cewa Hajiya tace ita zatayi mata kayan daki, da gani babu tambaya don tasan Babanta bazai iyayi mata irin wannan kayan ba.

CIGABAN LABARI

UMMASGHAR.

'YA'YAN MIJIStories to obsess over. Discover now