BABI NA GOMA

433 42 0
                                        


       'YA'YAN MIJI

Na Umm Asghar

               10
A haka dai rayuwa taci gaba, gashi Aisha har ta gama secondary school ta samu cigaba a makarantar Sa'adatu Rimi college of Education tana karantar catering wato fannin girke-girke.

A yammacin wata alhamis ne Aisha na kitchen tana taya Mami hidimar abincin dare, Mamin ce ta shigo kitchen din tace "sannu Aisha na tafi na barki da aiki ko, wai ina wajen Daddy muna maganar tafiya Umrah da zamuyi tunda yara suna hutu, inaga ko wajen jibi sai ki shirya ki koma wajen Hajiya kafin mu dawo tunda tafiyar zata kama ranar lahadi ne".

"Ashe tafiyar tazo, Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya. Mami ayi mana addu'a, In Sha Allahu zanyi shirin. Har kwana nawa zakuyi? "Inaga sati biyu ne" inji Mami.

Tunda Farida taji batun tafiyarsu Umrah taji kuma babu Aisha a tafiyar take ta faman yada mata da habaici. Ita kam Aisha ko kallonta batayi ba. Wani abu da Farida bata sani ba shine bata taba hada kanta dasu ba. Tasan matsayinta a gidan na 'yar cin arziki ta kuma san nasu matsayin na 'ya'yan gidan.

Wannan nema dalilin da yasa bata taba daga ido ta kalli wani abu da akayi musu da ba'ayi da itaba duk da dai Mami na kamantawa mawuyacin abu ne tayi musu wani abin batayi mata ba amma wasu lokutan tana yi din ita kuma Aisha hakan bai taba damunta ba.

A kowanne lokaci ta kasance mai godiyar Allah da bais ta zama mai kwadayin abin wani ba. Banda haka da tasha takacin Farida don kuwa sau tari Daddy yanayi musu kyauta ita da Ummie ba tare da ya hada da ita ba. Idan irin haka ta faru Farida ta dinga iyawa tana kafafa kenan duk don ta kular da ita.

Bata manta wani lokaci da Daddy yayi wata tafiya zuwa ingila ya kawowa su Ummie wayoyin hannu a matsyin tsarabarsu. Firirita da iyawar da Farida tayi mata a lokacin don ta kular da ita nada yawa. Ita kam ma dariya abn ya dinga bata don ganin ita dai wayar ma ba damunta tayi ba kuma ba wanda zata kira a waya gareta ba bare ta damu.

A yammacin asabar bayan ta gama hada kayanta zata tafi gidan Hajiya ne ta suka kasa don su kara yin sallama da Mami kafin ta wuce. Kowa na tambayarta abinda takeso su saya mata harda Zainab sai abinma ya bata dariya.

Da zata tafi ne Mami ta kawo kudi ta bata koda zata bukaci wani abu ba sai ta tambayi Hajiya ba. Godiya sosai tayi mata sannan ta dauki jakar kayanta ta kara yimata sallama ta fita. Har mota su Ummie suka rakata, ganin ta shiga mota sai Zainab ta fashe da kuka wai sai ta bita. Da kyar Ummie ta janyeta suka koma cikin gida.

Ta sani itama zatayi kewar Ruqaiya da Zainab sosai domin kuwa ta shaku da yaran ba kadan ba. Duk wata hidima tasu itace tun daga kan wankansu, cin abincinsu, shirinsu zuwa makaranta, kitsone da koya musu homework duk ita keyi. Mafi yawan lokuta ma tare suke kwana a dakin yaran.

Da sallama ta shiga cikin gidan tana janye da akwatinta. Baaba Indo mai aikin Hajiya na tsugune a bakin famfo tana wanke-wanke. Dagowa tayi tare da amsa sallamar tana cewa "maraba da takwara yanzu da yammannan kike tafe".

Cikin fara'ar da bata yankewa a fuskarta tace "eh Baaba Indo mun sameku lafiya" tace "lafiya lau hala dai zaki kwana mana biyu na ganki harda akwati". Aisha tace "eh sati biyu zanyi muku" tace "kai madalla kice muna da babbar bakuwa".

Murmushi kawai tayi ta wuce dakin Hajiya. Bata sameta a parlour ba sai ta wuce cikin dakin. A zaune akan sallaya ta tararda ita tana karatun AlQur'ani don haka akwatin kawai ta ajiye ta fito parlour ta zauna. Tayi kusan mintina goma a zaune kafin Hajiya ta fito daga dakin. Zamowa tayi daga kan kujerar ta gaisheta.

Bayan sun gama gaisawa ne Hajiya ke cemata taje kitchen ta debi abinci. "Wallahi na koshi Hajiya sai dai ko zuwa anjima" tace mata. Jefi-jefi suke hira da Hajiya har aka kira sallar magriba suka tashi don yin sallar.

Aisha dai bata tashi akan sallayar ba sai bayan da tayi sallar isha. Ko a gida ta saba bata tashi bayan magriba zama takeyi tayi tilawar karatun Alqur'ani har sai an kira sallar isha tukunna ta tashi tayi.

Bayan ta Isar ne ta fito ta debi abinci tana ci suna hira da Hajiya. Sallamar da Daddy yayi ne ya katse musu hirar da sukeyi. Yana zama Aisha ta gaisheshi ta tashi ta koma cikin daki taci gaba da cin abincinta.

Sallama ya shigo yayi wa Hajiya don jirginsu da safe zai tashi. Sun dade suna hira irinta tsakanin da da mahaifi.

Sosai yanda yake bawa Hajiya girmanta yake burgeta din kuwa kudinshi da mukaminshi basu saka ya banzatar da mahaifiyarshi ba, komai na jin dadin rayuwa ya wadata dashi.

UMMASGHAR.

'YA'YAN MIJIWhere stories live. Discover now