'YA'YAN MIJI
Na Umm Asghar
15
Tsaye take a kitchen tana shirya abincin dare. Tuwon semovita takeyi da miyar kuka. Ta gama tuka tuwon ta kwashe a cikin warmer ta kada miyar kenan Farida ta shigo kitchen din hannunta rike da farar roba irin wadda ake zuba yaji, tukunyar miyar ta bude ta juye abinda ke cikin robar.
Kallonta kawai Aisha ta tsaya yi tana mamakin irin wannan hali na Farida. Ganin zata fita daga kitchen dinne yasa ta mata magana tace "miye wannan kika zuba mini a miya Farida?" Murmushi ta saki wanda da an gani an san na mugunta ne tace "oh wannan, wani spice ne da zai karawa miyarki dandano, shinshina robar kiji" ta tura mata robar hancinta tana dariya.
Cikin takaici Aisha tace "wai lalle nebkika zuba mini a girki Farida". Dariyar shakiyanci tayi sannan ta juya ta bar kitchen din. Tsabar takaici Aisha ji tayi kamar tayi kuka.
Wulakancin Farida ya fara isarta, idan banda wulakanci ya za'ayi ta zuba mata lalle a cikin abinci da gangan. A yau dai kam bazata kyaleta ba don ta lura shirun da takeyi musu ne yasa suke yi mata abinda suka ga dama.
A yau dai kam sai taji dalilin irin wannan cin kashi da suke mata. Kashe cooker din tayi ta nufi parlour don taji dalilin Farida nayi mata abinda tayi.
Turus tayi ganin Daddy tare da duka yaran a cikin parlour din. Bata san cewa ya dawo gidan ba. Sannu da zuwa tace mishi a yayin da take karasawa cikin parlour. A takaice ya amsa mata da yauwa ba tare da ya dago ya kalleta ba.
Komawa tayi kitchen ta hado ruwa da kemo ta dora akan tray hadevda cups ta kawo mishi. Sida stool ta janyo gabanshi ta dora tray din akai tare da tsiyaya mishi ruwan a cup. Tana dagowa taga yaran duka na banko mata harara.
Dauke kanta tayi ta samu wuri ta zauna cikin sanyin jiki. Tana jinsu suna hira shi da yaranshi tamkar babu ita a wutin haka sukayi mata. Dama kuma idan da sabo yaci ace ta saba don idan suna wuri tazo ta zauna yi sukeyi tamkar basu san da zamanta ba.
Cikin muryar shagawaba Farida tace "Daddy me ka sayo mana ne tun dazu nake hararar ledojin daka shigo dasu", gaba daya suka saka dariya. Mu'azzam yace "eh wallahi nima dai hankalina yana kan ledojinnan". Murmushi yayi jin abinda suke cewa, mika musu kayan yayi yace gashinan kowa daya. Ga matan dai laces ne ya saya musu mazan kuma voile.
Gaba daya suka hau murna hade da yi mishi godiya. Duk da kyautar da aka musu idanun Farida na kan ledar dake aje a gefe. Cewa tayi "Daddy wannan kuma fa ko naka ne" a yayin da take daga ledar don taga abinda ke ciki.
Laces ne a ciki guda biyu sai dai da gani a idon ansan babu tambaya yafi wanda ya basu kyau da tsada. "Daddy nidai wannan nake so don yafi wancan kyau ko kuma ka hada mana gaba daya kawai". "Ajiye Farida wannan na Auntynku ne" yace mata.
Wani banzan kallo ta watsawa Aisha sannan tace "please Daddy wallahi tunda naga wadannan naji sun shiga raina don Allah" cikin murya irinta shagwababbun yara tayi maganar.
To shikenan ku dauka ita sai a saya mata wani" yace a lokacin da ya mike don hawa sama. Ihun murna Farida ta saka suka tafa da Ummie suna murna.
Ummie tace "amma gaskiya Farida kin burgeni ni ai bazan iya abinda kikayi ba, ko da yake dama ke Daddy's pet ce he never says no to you shi yasa kikeyin abinda kika ga dama".
Ta wani kada idanunta ta juyasu sannan tace "ato da ni din ta wasa ce, ai wallahi yarinya kadan ma ta gani idan dai nice. Ita har ta isa ta saka wannan lace din shima Daddy da taya bera bari. Ban gaya muku na kara mata maggi da gishiri a cikin miyarta bako, ai yau zakuci delicious".
Sai a likacin Aisha ta tuna da abinda Farida ta mata. Tashi tayi ta koma kitchen din don ta hada wata miyar tunda dai waccan ta lalace bazata ciwu ba. Tana jin Farida na gaya musu ai lalle ta zuba mata a cikin miya suna dariya.
A ranar wata asabar da dare ne suna zaune gaba dayansu a parlour suna kallo. Ita dai Aisha homework taje koyawa Zainab. Daddy ne ya shigo da sallama. Dukansu suka amsa suna mishi barka da shigowa. Ledar dake hannunshi ya ajiye akan center table yace yana mai kallon Aisha "ga nan nama" "mun gode Allah ya saka da alkhairi" tace mishi.
Bai zauna ba sama kawai wuce. Yana hayawa Farida tayi zirif ta dauke ledar naman ta nufi kitchen, tashi Ummie tayi tabi bayanta. Kwalowa Ruqaiya kira sukayi, tashi tayi taje amsa kiran da sukayi mata.
Sai gata ta dawo da plates guda biyu a hannunta ta mikawa Yaya Khalifa da Mu'azzam sannan ta koma ta dauko nasu ita da Zainab. Tare suka fito dasu Ummie suma da nasu plate din a hannu.
Wato kenan su sukayi rabon naman ta kuma tabbata basuyi rabon da ita ba. Ko kallonsu batayi ba ta tashi taje ta hada kayan abincin Daddy ta nufi sama don bata tsammanin zai kuma saukowa.
Bata sameshi a parlour ba don haka ta wuce cikin dakin. A kwance'akan gado ta iske shi. "Daddy ga abincinka" tace mishi a lokacin da take ajiye tray din a kasa. Tashi yayi zaue sannan yace "kinga kwashe abincinnan ki kawo mini tea kawai sai ki hado mini da naman".
Tsaye tayi a wurin ta kasa gaba ta kasa baya ta kuma kasa gaya mishi cewa babu naman ya kare. Cikin daga murya yace "kinyi mini tsaye a ka bazaki kawo mini bane ko me"?
Cikin fargabar abinda zaice tace mishi "babu naman ne ya kare". "Ban gane da babu ya kare ba, kina nufin gaba daya kuka cinye ba tare da kin dibar mini ba. Ke wacce irin yarinya ce kwata-kwata bakida common sense baki san abinda ya dace ba".
Ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba, fada kawai yakeyi kamar dama irin kiris dinnan yake jira. Sai da ya gaji don kanshi sannan yayi shiru. Hakuri kawai ta bashi ta sunkuya ta debi kwanukanta ta fita daga dakin.
Ajiye kayan tayi ta bude freezer ta fito da naman rago ta yankashi sirarata wanke ta dora a wuta. Sannan ta fito da dakakken kuli-kuli da tomatoes da attaruhu da albasa ta gyara. Tsiren tukunya ta hada mishi sannan ta dafa tea ta zuba a flask ta shirya cikin tray tana jiran naman ya karasa ta sauke.
Koda ta duba taga ya nuna sai ta sauke ta zuba a cikin bowl ta hada akan tray din. Tana cikin wanke tukunyar da tayi amfani da ne taji muryar Ummie a bayanta tana cewa "Farida gane mini ikon Allah, wai matarnan nama tazo ta gasa don bata samu taci wanda Daddy ya kawo ba.
Farida ce ta karaso kitchen din tace "ai kinsan duk wanda bai taso cikin arziki ba idan ya sameshi daga baya cin kwan makauniya yakeyi mishi". Hannunta ta kai zata dauki naman, Aisha tayi caraf ta rike hannun tace "wannan ne kuma baki isa ba, kun rabe wancan a tsakaninku kun cinye ban tanka muku ba ba kuma zakuzi kuce zakuci wannan ba. Duk wacce take so ta bude fridge ta dauka ta dafa amma ba wannan ba".
"Samun wuri, ke nan har kin isa muna son abu kice baza mu dauka. Naga dai ubanmu ne ya sayi kayan ba na wani ba" cewar Ummie kenan. Aisha dai ta kankane namanta ta hanasu tabawa tacec"kome zakuce ku fada nama ne dai bazaku taba mini ba".
Suna cikin hayaniya ne suka ji gyaran muryar Daddy. Gaba daya sai suka shiga taitayinsu don fuskarshi sam babu annuri. "Lafiya kuke mini hayaniya a gida da darennan, ke kuma bazaki kawo mini tea din bane" yace yana maida kallonshi ga Aisha. "Kayi hakuri yanzu zan kawo" tace tana mai daukar tray din.
Ya juya zai bar kitchen din kenan Farida tace"Daddy kaga wai nama muka gani muna so wai bazata nbau ba". Juyowa yayi ya kalleta yace "nama wane iri ba kince babu ba kun cinye". Cikin muryarta mai sanyi tace "eh wancan babu wani ne nayi maka dama".
Yace "kuma shine bazaki basu ba alhalin suna so, to a wanne dalilin. Ku dauka kuje kuci ni bana ci" yace wa su Farida. Bayan ya fita daga kitchen dinne suka kyalkyale da dariya Ummie tace "wayaga cusa kai babu kwarjini".
Ajiye musu bowl din naman tayi ta wuce ta kai mishi kayan tea din ranta a matukar bace. Don takaici a daren har kuka sai da tayi.
UMMASGHAR.
ESTÁS LEYENDO
'YA'YAN MIJI
Ficción GeneralAisha yarinya ce da rikonta ya dawo hannunta Goggonta bayan rasuwar mahaifiyarta inda ita kuma ta mika ta ga matar danta. Rayuwa ta juyawa Aisha baya ne a lokacin da marikiyarta ta rasu aka aura mata mijin marikiyarta.
