Da hanzari tabi bayanta tana kwalla mata kira, "Hafsah! Zo nan, dawo karkije ki fadi!" Da dariya take maganar tana bin bayan yarinyar. Tunda take a rayuwarta, tun bayan da Hanan ta rasu Lubnah kuma ta kawota gidansu bata taba irin wannan farin cikin ba. Ita duk aikin da Hafsar ma ta saka ta ba damunta yayi ba, ganinta da tayi, wasan da sukayi tare, rigima da komai da komai ya wadace ta.
Sannan barna irinta Hafsah na dan zaman da sukayi yasa ta bita itama da dan gudunta. Hanyar garden din gidan taga ta nufa, binta take tana kiran sunanta amma Hafsah wasanta kawai takeyi. Koda ta isa garden din ganinta tayi zaune saman cinyar Rayyan, ita gabanta ma har faduwa yayi, dan ta manta yaushe rabon data ganshi cikin gidan.
Ganin Lubnah na wajen itama zaune yasa ta taka ta isa wajen, "Yi hakuri dan Allah, Hafsah tashi muje." Ta mika hannu da niyyar tazo su tafi amma yarinya ta mak'e kafada, dama abu Rayyan yake nuna mata a wayarshi.
"Emma nakeso naga ko taci abinci yau, Ammi. Nasan Abba bai bata abinci ba, kila ma har wanka tanaso tayi kuma bai mata ba." Hafsah ce ke magana ko kallon inda Ramlah take ma batayi, idonta kyam akan Rayyan dake kokarin mata downloading My Emma a wayarshi.
"Su Ramlah fa anyi diya, ban taba ganin dariyarku irin ta yau ba. Yaushe Dr Aliyu zaizo daukarta? Ko sai dare? Kila ma ya bar maki ita ta maki weekends ko?" Lubnah ce ke magana da sigar wasa tana yar dariya, wanda itama Ramlah ta mayar mata da dariyar da takeyi.
"Aa fah, anjima kadan zaizo daukarta. Gidan iyayen mamarta zasu kaita ma wannan short term break din, yace mun ta kwana biyu bataje ba." Abunda ta furta kenan tana murmushi sannan ta koma wajen Hafsah.
"Taso muje Hafsah kinji? Kinga ko ya maki downloading Emma din ba taki bace ba, muje na maki da wayata." Da kamar bazata taso ba sai kuma ta taso a hankali tana kallon Rayyn dake mata murmushi.
"Idan na kara zuwa zan ganka?" Abunda ta tambaya kenan da irin kallon alkawarin nan na yara.
Murmushi yayi ya shafa mata kai, "Eh Hafsah, kafin ki dawo zansa wannan Emma din ta girma sai suyi kawance da taki, kinaso ko?"
"Eh inaso. Bye!" Hannunta da Ramlah ta janyo yasa ta mashi waving da dan murmushinta da haka Ramlah ta jata suka tafi dakinta.
Zama sukayi kan gadonta ta janyo wayarta tana mata downloading my emma ita kuma sai bata labari take. Ji takeyi kamar tare take da Hanan bawai Hafsah ba. Bayan ta gama mata downloading suka zauna suna game din, Hafsah sai korafi take akan wai wannan jaririya ce, ita diyarta ta zama yar budurwa. Saida Ramlah ta mata alkawari cewar zata rikayi har ta maidata yan mata kafin ta kara dawowa.
Har saida sukaci abinci dare a daki tare sannan taga kiran Dr Aliyu ya shigo wayarta. Dauka tayi yace mata yana kofar gida kafin ta tashi ta kimtsa Hafsah da ledar kayan zak'in data kwasa mata gaba daya suka sauka kasa. Saida Hafsah tama Lubnah da Mama kafin tana hannunta suka fita waje.
Hangoshi tayi ya jingina da motarshi yana kallon kofa alamar jiran fitowarsu yakeyi. Da murmushi suka karasa wajen motar. Da gudu Hafsah ta ruga ta rungumeshi tana ihun murnar ganinshi, "Abba nah!"
Dukawa yayi ya kawo daidai tsayinta yana murmushi, "Na'am diyar Abban ta, kinyi kewar Abbanki ko?"
Dariya tayi ta rungume shi, "Na danyi kadan, amma Ammi bata bari nayi da yawa ba." Har zaiyi magana tayi saurin tareshi, "Abba, ina my Emma dita? Ka bata abinci? Ka mata wanka?"
Dariya yayi ya mike tsaye yana ciro wayarshi daga aljihu, "Naga dai tanara magana wai wanka takeso kuma tanajin yunwa, amma Hafsah ban iya ba. Yanzu dai ga wayar ki shiga mota kiyi zanyi magana da Ammin ki, kinji?" Koda yace Ammi saidai yaji maganar wani iri, da hanzari ta karbi wayar ta shiga mota shi kuma ya karasa inda Ramlah tayi tsaye tana kallonsu da murmushi akan fuskarta.

KAMU SEDANG MEMBACA
MIJINA NE! ✅
RomansaAshe dama ana mutuwa a dawo? Ashe dama in mutum ya mutu, aka binne shi a kasa zaka iya ganinshi a rayuwarka? Kodai idonta ke mata gizo? Ko kuwa ta haukace ne? Aa, kila kuma kuncin da rayuwarta take ciki shine take ganin mutanen daya kamata ace tana...