23-25

965 32 1
                                    

❄️❄️❄️❄️❄️
*Ḧ̤Ï̤B̤̈B̤̈Ä̤T̤̈Ṳ̈L̤̈L̤̈Ä̤Ḧ̤*
❄️❄️❄️❄️❄️

*°•(ĸyaυтa daga Aℓℓαн)•°*

*°•ιиιqυιту,ємραтну,нυмιℓιαтισи & яσмαитι¢ ℓσνє💑•°*

*MALLAKAR:HAFSAT HAFNAN💕*

*WATTPAD:HAFNANCY*

https://m.facebook.com/Hafnans-Novell-246747739535534/

*°•ѕα∂αυкαяωα gα Dr. υмαя fαяυq вαнαgσ,ємιя σf иιgєя ѕтαтє мιииα•°*

*°•ιnтellιgenт wrιтer'ѕ aѕѕo✍•°*

https://m.facebook.com/Intelligent-Writes-ASSO-294634797868361/
__________________________________
💥

*NOT EDITED*

*Թɑցҽ 23-25*

_________*'TEWI'* wani dan karamin ƙauye ne dake ƙarkashin *'BOSSO lOCAL GOVERNMENT'* wanda ke ah jihar *'MINNA'* .Tewi ƙauye ne sosai wanda wutar lantarki ta Nepa ma basu dashi,ƙauye ne wanda beyi wani suna ba sabida Karancin mutanen ciki,mutanen wannan kauyen ko dari shidda basu kai ba,Allah ya albarqaci ƙauyen Tewi da kasar noma,shukunansu nan da nan suke girma,hakanan zaka gan ganyayyakin fresh dasu abin gwanin ban sha'awa dai.Yaren da akafi yi shine *'GWARANCI'* kasancewarsu gwarawa.Sunan mai unguwar wannan ƙauyen *'MAL.MUHAMMADU NAZIRU'*.Shugaba ne mai kirkin gaske da kuma taimako saidai kuma beyi sa'an matan aure ba.

*°•GIDAN MAL.MUHAMMADU NASIRU•°*

Uwale wacce ta kasance amaryar Mal.Muhammadu ce ta bada himma wajen dakar dawa dake acikin wani katoton turmi ayayin da uwargida ran gida mai mulki wato Mariya take zaune akan kujera 'yar tsugunno tana tankad'e wanda Uwale ta riga ta daka,sai taga yayi lukwi dashi kafin ta juye awani kafcecen kwano mai dan zurfi da kuma fadi.

Can Uwale ta dakata tare da sanya hannu daya ta rike ƙwanƙwasonta,dayan kuma rike da tabarya,yamutsa fuska tayi wanda ya nuna alamun gajiya atattare da ita.

Mariya ta dago kai ta kalleta jin tayi shiru da dakar,ganin yanayinta yasa ta dan murmusa tace"Yadai Uwale kin gaji koh?"

Uwale tace"washhh! Yayah Mariya wallahi ƙwanƙwasona kamar zai karye,Allah na gaji don Allah zoki karashe ni kuma na cigaba da tankad'en ko kuma aƙira Fulani ta ƙarashe......"

Saurin dafe ƙirji Mariya tayi,cikin daga murya tace"Wah zai kira Fulani anan?ke tunda ma ta soma yoyon fitsarinta kin sake ganin na bata aiki ta min?Ni Mariya bazan ci kazanta ma don haka ni bani tabarya na karashe idan da gaske kin gajin ne...." Ta mike ta kwace tabaryar ahannun Uwale wacce tunda Mariya ta soma maganarta take ta tikar dariya son ranta.

Tace"Kai Yayah baki da sauki in har akan Fulani ce...."

Ko kala Mariya bata ce mata ba illa maida hankali da tayi akan dakarta.Jan jiki tayi xuwa ga kujerar da Mariyar ta tashi,ta cigaba da tankad'en.

Fulani kuwa dake can dakinta taji duka hirarsu akanta,wani hawaye masu dumi suka gangaro mata saman kunci,da sauri ta sanya bayan hannunta ta daukesu,cikin rawar murya ta daga hannunta sama tace"Yah Allah! na rokeka ka kubutar dani daga hannun wa'ennan azzaluman matan,nasan da nawa laifin aciki amma Yah Allah ka karkato da hankalin Muhammadu gareni ya maidani gaban iyayena...." Kuka yaci ƙarfinta,takai hannu tana shafa fuskar 'yar 3days old baby dinta,ahankali tace"'Yata don Allah ki yafemin don duk nice silar shigowarki cikin wannan kuncin rayuwar,baki san komai ba amma har kin soma dandanar dacin rayuwa....."

HIBBATULLAH Where stories live. Discover now