🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️
*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_
*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''
*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈
*\F.W.A📚/*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._
*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER Eleven*
________🎓 A parking lot yayi parking ɗin motan sa sannan yafito saƙale da briafcase ɗin sa a kafaɗa yanufi cikin gidan
Yana shiga parlour'n da sallama a bakin sa
Saleema tafito cikin ɗakin ta riƙe da waya, amsa masa tayi tana kallon sa cike da fara'a a face ɗinta sannan tanufe sa, jakan hannun sa ta'amsa tana mishi sannu da zuwa
Amsa mata yayi yana ɗan guntun murmushi
Har ta juya yariƙo hannun ta suka jera tare cikin ɗakin
A gaban gadon suka tsaya ta'ajiye masa jakan tana shirin janye hannun ta yasake riƙe wa yana kallon ta, don haka bata yi yunƙurin sake janye wa ba tatsaya tana kallon sa cike da so
Murmushi yasakar mata yana zama kan gadon kafin yajanyo ta ya'aza ta kan jinyan sa yana faɗin "yau Halwa taje school kenan tabar min matata ita kaɗai da kewa ko?"
Murmushi Saleema tayi tana ɗan gyaɗa masa kai cike da kunyan sa
Numfashi yaja yana lumshe idanun sa kafin yabuɗe akan ta, yanda yake mata wani irin kallon ƙurilla hakan yasa tayi saurin cewa
"Uhmm abincin ka.. in kawo maka nan?".
Shiru yayi kamar bazai ce komi ba har alokacin idanun sa na yawo ajikin ta, ahankali yaɗan matso da kansa kusa da fuskarta yaraɗa mata
"Saiiiii nayiii wanka zan ciiiiii..."
Yanda yayi maganar cikin jan kalmomin hakan yasa tsigan jikin ta miƙe wa, tayi saurin ɗaga kanta hakan yasa kansu yahaɗe waje ɗaya
Dasauri yaɗan ja baya da nasa yana yarfe hannu cikin shagwaɓe fuska tare da runtse idanu yace "zaki fasa min kai ne?"
Yanda yayi maganar yasa ta yin dariya itama tana sosa goshin ta tace "ya haƙuri ban kula ba".
Taɓe baki yayi kafin yace "sai na rama".
Kafin ma tayi magana ya ɗaura hannun sa akanta yazame ɗankwalin dake kan ta, sannan yamayar da hannayen nasa bayan ta yasoma jan zip ɗin rigan yana faɗin "bari muyi wanka tare ko?"
Murmushi Saleema tayi tana Sad da kanta ƙasa
Sai da yagama zage mata zip ɗin kafin yasake faɗin "zamu je gidan Bro.. Aamir yana fama da zazzaɓi, zuwa yaushe Halwa zata dawo?"
YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a
