🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
'''{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}'''*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''.
*CHAPTER 12*
Tana fitowa suka haɗa idanu da Yazeed da yake jingine jikin motan sa, tun sanda tafito yasoma murmushi har ta ƙari so wajen sa da sallama a bakin ta, amsa mata yayi still yana murmushi yace
"Barka da fitowa gimbiyar Mata kyakykyawar yarinya".
Murmushi tayi tace "fatan kazo lafiya?"
Yace "tun sanda dai muka haɗu dake ban sake jin lafiya ajikina ba, har kuwa fitowar da nayi daga gida nazo gare ki, but yanzu da nagan ki agabana sai naji kamar an kwaso duk lafiyan mutanen duniya ne an ɗaura min ni kaɗai, kinga kuwa yanzu zan iya ce miki lafiya ƙalau kenan".
Murmusawa tayi tana kallon shi tace
"Na kula dai kai ɗin nan kana da son wasa da yawa".
Shima murmushin yayi yace
"Gaskiya ne ƴan mata, to fatan kina lafiya kema? Ya su Mama da kowa da kowa? Kinga ban zo ba sai yau ko? Wlh kwana biyun nan aiki ne yayi min yawa, amma baki ji yanda na azabtu ba da rashin ki, ji nake kamar na shekara ɗari tare dake, sosai nashiga damuwa Burina kawai nazo nasake tozali da kyakykyawar fuskar nan taki".
Ita dai batace komi ba sai murmushi da take yi
"Ƴan mata da fatan dai za'a bani matsuguni acikin zuciyar ki, wlh sosai nakamu da ƙaunar ki, ina fata dai babu wanda yariga ni?"
Halwa tace "ai tun farko kamar in ban manta ba sai da nafaɗa maka ni ɗin mallakin wani ne, sai dai in baka haƙuri Malam Yazeed domin ma fitowan nan da nayi nazo ne nasanar maka an riga da anyi min miji".
Cikin fuskar damuwa yace
"Dan Allah wai dagaske kike yi?"
"Wlh dagske nake maka, ina da mijin aure kuma nan ba da daɗewa ba za'a sanya mana ranan aure ni dashi".
Cike da rashin jin daɗi Yazeed yace
"Yanzu shikenan wani ya rigani? Shikenan kina nufin zan rasa ki? Wlh Halwa sosai na kamu da ƙaunar ki a lokaci guda, yanzu kuma bansan ya zanyi in cire son ki cikin zuciyata ba".
Cike da tausayin sa saboda sosai tayarda dashi kuma ta ga tsantsan gaskiyar sa a fuskar sa tace
"Kayi haƙuri a sannu zaka manta dani ai, dama baka daɗe da sani na ba, don haka insha Allahu nan ba da jimawa ba zaka neme ni karasa ko tuna ni bazaka sake yi ba".
Ɗan murmushin gefen baki yasaki yace
"Kayya a naki fahimtar kenan Halwa, wlh bakisan yanda nake jin ki cikin zuciyata bane zai yi wuya nacire ki sabida ƙaunar da nake miki ya wuce tunanin ki, ni kinga ban iya saka abu cikin rai ba, kuma zan faɗamiki gaskiya ta kece macen da nafara so nafara kulawa a matsayin wacce nake ƙauna, taya kike tunanin lokaci ɗaya kuma zan inya manta ki?"

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a