🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuDahirah*👈 _WhatsApp Number 07065334256_
*\F.W.A📚/*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._''''Allah ya dawo dani mu tsunduma cikin labarin
Na gode masoyana.'''
*BOOK TWO*
.
_______________________________
*CHAPTER One*
________🎓Suna zaune su Biyu akan dainning table suna cin abinci
Halwa kai abincin bakin ta tayi tana lumshe idanun ta cike da jindaɗi, sai kuma tabuɗe idanun taɗaura akan Saleema da itama tamayar da hankali wajen cin abincin ta, murmushi me sauti Halwa tasaki still tana kallon ta tace
"Sister gaskiya abincin nan kamar zai tsinke min kunnuwa, kina gani fa har rawa suke yi sabida tsaban daɗin abincin nan".
Dariya Saleema tasaki tana kallon Halwa da taƙara ɗibo wani abincin takai bakin ta tana faman lumshe idanu
"Bari dai in tashi in ɗauko pilow in tare ki dashi, idan ba haka ba babu me iya tare ki nan gaba in kikaci gaba da wannan santin".
"Allah Sister ba santi bane, kinji yanda abincin yake da matuƙar daɗi ne sai kace wacce tadaɗe da ƙwarewa, wlh ko Ni bazan iya rin wannan ba".
Murmushi Saleema tayi cike da jindaɗi sai dai bata iya cewa komi ba
"Ƙara min miyan". Halwa tace hakan tana miƙo mata plate ɗin shinkafan
Zuba mata miyan tayi tana faɗin "Kinsan jiya da Zazzaɓi Husna ta kwana, wlh duk na ruɗe sabida yanda naga tana yi, da ba don Yaya Barrister ba bansan yanda zan yi ba, shi yatashi yayi ta rarrashin ta har yana cewa in koma in kwanta". Taƙarishe maganar nata tana wani irin murmushi me ma'anoni da yawa wanda Ni kaina bangane mata ba
Shiru Halwa tayi bata ce komi ba illa kai abinci bakin ta da take yi
Ɗago kanta Saleema tayi takalli Halwan sai kuma tamayar da kanta kan abincin tana sake yin murmushi
Tasan da cewa baza ta taɓa tankawa ba, halin ko in kula shi Halwa ke nuna wa Husna, tunda tahaife ta ko ɗaukan ta idan ba ya zama dole bane to ko kallo bata ishe ta ba, baza ka taɓa tunanin itace uwarta ba
Basu sake magana ba har sanda suka gama cin abincin suka koma parlour, Hira suka ɓarke dashi cike da nishaɗi, sai da aka kira sallah kafin Saleema tashige ɗaki don yin Sallah, ita kuma Halwa tadasa Kallo kasancewar bata sallah
Khalil ne yaturo ƙofan da sallama a bakin sa hakan yasa Halwa ɗago idanuwan ta tasauke acikin nashi idanun wanda yayi dai-dai da yankewar gaban su a lokaci ɗaya

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomansaLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a