Part 7

84 7 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

⚖️ *FEENAH WRITER'S ASSO📚*
'''{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *⚜{{F.W.A📚}}*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 7*

Ahankali yake taka motan kamar koda yaushe, wayan sa dake ajiye ne tasoma ringing, hannu ɗaya yamiƙa yaɗau wayan bayan da yaduba yaga me kira, picking call ɗin yayi tare da saka ta a speaker 🔊 yamaida ya'ajiye

"Hello Bro".

Daga can Sameer yace

"Kana ina da Allah?"

"Yanzu gani na taso wajen aiki zan koma gida".

Sameer yace "yauwa kazo kaɗauke ni Please, motata ce tasami matsala an tafi da ita, ina office Ina jiran ka".

"Ok ganinan".

Juya kambun motan yayi yasauya hanya, minti 15 yakawo shi babban asibitin da Sameer yake aiki, bayan yayi packing fitowa yayi yashiga cikin asibitin, direct office ɗin Sameer yazarce, yana shiga yaganshi zaune yana cike wasu takardu, hannu yabasa suka gaisa sannan yasami waje yazauna

Sameer yace "just give me 10 mint don Allah yanzu zan ƙarisa sai mutafi".

"Babu Matsala". Khalil ɗin yafaɗa yana gyara zaman shi kan kujeran yalumshe idanun sa

"Ka gaji ko?"

Ɗan yamutsa face ɗin sa yayi ba tare da ya buɗe idanun sa ba yace

"Sosai ma, barci kawai nake ji wlh yanzu".

Ɗan kallon sa Sameer yayi yace

"Wai ya maganar tafiyan ka ne? Har yanzu banji kace komi ba?"

Idanuwan sa yabuɗe yana kallon Sameer ɗin yace

"Zuwa Friday zan tafi".

Jinjina kai yayi yace

"But Yakamata kayi taka tsantsan kasan Alhaji Mubarak ba ƙaramin mutum bane, don bani da shakka duk abun da kake shirya wa ana sanar masa, Ni yanzu maganar ma da nake so nayi maka kan Nazeefa ce, Yakamata kaciro ta daga wannan gidan kakaita wajen Mom hakan zai fi".

Khalil yace "ai jiyan nan naɗauko ta namaida ita gida na, inaga can zata zauna".

"Kana ganin babu Matsala?" Cewar Sameer

Gyaɗa masa kai kawai yayi

"Ok amma dai Yakamata kaƙara masu gadi, don nafi tunanin in har tana gidan ka zasu fi sanin haka, sannan kuma kaga kai tafiya zakayi Yakamata kaduba shawarata".

Shiru Khalil yayi naɗan wasu sokonni kafin yace

"Ok Bro".

Daga haka hira suka soma duk dai akan case ɗin Alhaji Mubarak, kafin Sameer yagama suka tashi suka fice, har gidan sa yasauke sa Sameer ɗin yace

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now