chapter Twenty Nine

89 5 0
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Twenty Nine*

________🎓 *ONE WEEK AGO*

   Suna zazzaune akan dainning table suna yin breakfast wayan Haris tayi ƙara, sai da yakai Cofin shayin sa baki yakurɓa kafin yakalli wayan, ganin sunan Dady yafito ɓaro-ɓaro sai yayi saurin ajiye Cup ɗin yana kai hannu yaɗauki wayan tare da yin peacking yana karawa a kunne

"Aslm alaikum Dady.."

"Eh Dady ban fita ba but yanzu zan fita".

"Ok to".

Cire wayan yayi daga kunnen sa yaɗau tissue yana share bakin sa, be ce komi ba sai da yamiƙe yajanye kujeran da yatashi sannan ya dube su yace

"Ni zan wuce but bazan dawo ba yau sai zuwa dare insha Allahu sabida akwai inda zan je".

Miƙe wa Zubaida tayi don ta rakasa, yayinda Fahima tayi masa adawo lafiya tana ci gaba da breakfast ɗin ta

Har bakin ƙofan Parlour takai sa kafin tamiƙa masa briafcase ɗin sa suka yi sallama yafice

Mota yahau sai Family House ɗin su domin amsa kiran Dady da yayi masa.

     Bayan ya shiga da motan sa tanƙamemen gidan nasu wanda yakasance me tsananin kyau da burge wa, duk da iyayen sa kaɗai ne agidan ada, but a yanzu Daddyn nasa ya dawo da ƙannin sa biyu da iyalan su suna zaune agidan, kasancewar su kaɗai Allah yaba ma iyayen su that's why mahaifin Haris ke ji dasu sosai, shiyasa da yadena siyasa a yanzu sai yagina wannan tanƙamemen gidan kuma yayi musu umarnin dawowa kowanne da nasa Part ɗin.

      Fitowa yayi a motan yanufi cikin gidan, koda yashiga parlour'n; Daddyn sa ne da Mamyn sa zaune cikin damuwa, shi kansa Haris da yashigo ya tabbatar ba lafiya ba ganin yanda sukai tsamo-tsamo fuska duk babu walwala, gaishe su yayi suka amsa masa

Dady ne yadube sa fuskan sa da damuwa yace, "Haris".

"Na'am Dady". Ya'amsa masa ahankali yana kallon sa

Numfashi yaja kafin yace, "wacece Halwa?"

Wani irin bugawa gaban Haris yayi jin sunan Halwan, still sake tsatstsare Dadyn da idanu yayi ya kasa furta komi

"Kayi shiru ina magana?"

"Alhaji na fa faɗa maka kamar yarinyan nan ce da yayi haukan son ta har yakwanta a Hospital". Cewar Mamy idanun ta na kan Dadyn

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now