🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''.
*CHAPTER 26*
Tunda suka fito daga asibitin suka shiga cikin keke napep Halwa take faman kuka, duk ta takure waje ɗaya ta rufe fuskarta da Hijab, Mama kuwa itama tunda tazauna taɗauke kai gefe, maganganun Doctor kawai suke dawo mata cikin kunnen ta, zuciyar ta sai wani irin tafarfasa take yi ƙiris take jira, suna kai wa tasauka tabashi kuɗin shi tashige gida dasauri, Halwa kuwa ahankali tasauko tanufi gidan nasu, sai dai takasa shiga ciki sai tatsaya a zaure tana ta kuka, tana nan tsaye a wajen sai ga Baba da Nura sun shigo atare, suna ganin ta sukasan babu lafiya, domin Mama takira su a waya tace su dawo yanzu, kuma bata faɗa musu abinda ke faruwa ba, Baba ne yasoma cewa
"Halwa me kike yi anan? Me yafaru ne?"
Bata ɗago kai ba sai ma ƙara volume ɗin kukan ta da tayi, nan da nan jikinta yasoma rawa kamar an sakata a shocking, Nura zuwa yayi yariƙo ta yana faɗin
"Lafiya Halwa? Menene haka wa yabige ki?"
Still shima shiru tayi masa
Baba yace "Nura taho da ita mushiga gidan sai muji ba'asi wajen Maman taku".
Riƙo ta kuwa Nura yayi, babu musu tabi shi suka shiga ciki, ɗakin Mama suka nufa gaba ɗayan su, Mama na zaune tana faman hawaye suka shigo, abinda yaƙara ɗaure musu kai kenan suka hau tambayan ta "lafiya?" Hankalin su duk atashe, but Mama taƙi tayi magana sai Hawayen ta take yi, zama Baba yayi gefen ta yayinda Nura ma yasamu waje yazauna yajanyo hannun Halwa itama tazauna kusa dashi
Baba yace "wai Hauwa lafiya muka ganku a wannan yanayin? Meke faruwa ne kiyi mana bayani?"
Ɗago kan ta tayi cikin baƙin ciki tace
"Wani bayani kakeso kaji Baban Nura? Ace wai yau Halwa ce tayo mana ciki agida, cikin shege fa Halwa tayi a gidan nan". Sai tasake fashewa da kuka
Atare Baba da Nura suka maimaita cikin Shegen, Nura har da ja da baya yana matsawa kusa da ita, cikin kaɗuwa Baba yakalli Halwa da har yanzu takasa buɗe idanun ta yace
"Dagaske ne cikin Shege kikayo min agida?"
Shiru Halwa tayi
"To ya za'a yi tafaɗa maka? yanzu muka dawo daga asibiti likita yatabbatar mana tana ɗauke da cikin Shege acikin ta, to wlh tallahi ba dai nan gidan ba, bazai taɓa saɓuwa ki haifa mana ɗan Shege agidan nan ba, duk gatan da mukayi miki Halwa kikasa saka mana da abun kirki sai abun tsiya? ashe duk zaman da muke yi dake amanar mu kike ci mu duk bamu sani ba? To baza mu ga wannan abun kunyan ba dole ki koma can dangin mahaifin ki tunda bakisan halacci ba, na rabo ki da can ne don naga kina shan wahala amma kin nuna mana ke ba mutumiyar arziƙi bace".

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a