🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📚*
'''{{Ɗaya tamkar da Dubu💪}}'''*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*⚜{{F.W.A📚}}*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''.
*CHAPTER 8*
Tafiya suke yi suna sanye da uniform, fitowan su kenan akan hanyan su tazuwa school, Halwa take bata labarin haɗuwan su da Yazeed jiya, ita kuma Zainab zai ɓaɓɓaka dariya take yi har da riƙe ciki
"Ke kiyi fa ahankali karki jawo mana mutane nan". Cewar Halwa kenan tana kallon Zainab
"Ƙyale ni in dara, wlh kin bani dariya, hhhhh wai ke adole ga kurma, kai wlh banji daɗi ba da bana nan akai wannan draman, kawai lokaci ɗaya Allah yatoni asirin ki".
Sai takuma kwashewa da dariya, Halwa bige mata kafaɗa tayi tana faɗin
"Ke fa tsiyata dake ba'a zancen arziƙi dake, yanzu sai kihau ma mutane wannan haukan naki, mtswww".
Taja gajeren tsaki tana ɗaure fuska, sai lokacin Zainab taɗan sassauta dariyan da take yi tace
"Wooo kurma ta Yazeed yi haƙuri ban sakewa".
Wani irin kallo tayi mata tace
"Gyara kalaman ki, kidena danganta ni dashi, kinsan dacewa ni ɗin mallakin Yaya Nura ne shi kaɗai, to dan Allah kidena bana so".
Taɓe baki Zainab tayi tace
"Nafi kowa sanin haka ai, amma babu yanda Allah baya lamarin sa, yanzu sai kiga an sauya d.."
Saurin bige mata baki Halwa tayi tana faɗin
"Kull.. karki soma, wlh in kika ƙarisa sai an ji mu dani dake, Allah ni nakula ma kamar baƙin ciki kike min, to ta Allah ba ta ki ba, insha Allahu sai na zama mallakin Yaya Nura na sai dai kimutu".
Zainab dariya tayi tace
"Hmmm yi haƙuri ƙawalli na dena, in kinso ma gobe aɗaura miki aure dake dashi, ni wlh bata shafen ba".
Halwa tace "to ai ko bakice ba, ni inda za'abi ta shawarata wlh kafin muƙarisa wannan makarantan kawai aɗaura mana aure, domin ni a tsarina bana son nagama secondary batare da nashiga daga ciki ba".
Baki Zainab tariƙe tana kallon ta
"Lallai Halwa kin ƙosa da yawa, amma bansan haka ba sai yanzu, to gaskiya Yakamata su Mama suyi saurin miƙa ki tun kafin aji sautin kiɗan ya sauya".
"Ni da ma zaki taimaka min da yafi, kije kisanar mata tunda su har yanzu sun kasa sanin haka, wlh Zainab ina faɗamiki auren wuri daɗi ne dashi, kema dai ki aje wannan aƙidan naki kawai mu jone ayi mana tare ko ma huta, ko ba haka ba?" Cewar Halwa tana kallon Zainab tare da ɗage mata gira

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a