chapter Twenty Six

68 4 0
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Twenty Six*

________🎓Kamar yanda Halwa tafaɗa mata address ɗin gidan su Saleema can tanufa, a cikin motan babu me magana, ita dai Halwa kallon hanya kawai take yi tana kitsa abubuwa aranta da tunanin abinda zai faru idan takoma..

Ƙaran horn ɗin da Mami ta danna ne yadawo da ita hayyacin ta, takai duban ta ga Gate ɗin lokacin har me gadi ya leƙo don ganin wanene, be buɗe musu ba sai da yazo har wajen motan yayinda Mami tasauke Glasses Motan

Har ya buɗe baki da ninyan yin magana sai yahangi Halwa, cike da tsagwaron murna da al'ajabin ganin ta don zuwa yanzu har ma'aikatan gidan sun san abunda yafaru duba da yanda iyayen gidan nasu hankalin su yake a matuƙar tashe da halin da Saleeman ke ciki

Washe baki yayi yace "Hajiya Halwa ke ce?"

Murmushi tayi masa cikin sanyin murya tace "eh Yusha'u".

"Masha Allah bari in buɗe muku ƙofan to". Yayi maganar yana nufan Gate ɗin dasauri har da haɗa wa da gudu

Yana shiga yabuɗe musu Mami taja motan zuwa ciki

Har wajen motan me gadin yabi su bayan da yamayar da Gate ɗin yarufe, anan ne suka gaisa da Mami itama Halwa tagaishe sa sannan sukai ciki

Halwa ce agaba don haka ita tabuɗe ƙofan tashiga da sallama a bakin ta

Ummi dake zaune saman kujera ta riƙe waya a hannu tana latsawa, kallo ɗaya kayi mata zaka hango tsantsan damuwar da take ciki

Sallaman Halwan shine yasa taɗago kai sabida jin muryan da bata taɓa zaton ji ɗin ba a halin yanzu, dasauri tamiƙe ganin dai itan ce zuciyarta cike da zallan mamaki tare da wani irin murna

"Halwa.." takira sunan ta idanun ta akanta don tama kasa motsawa

Murmushi Halwa tayi takalli Mami dake bayan ta, sai kuma tasad da kanta ƙasa

Mami gaba tayi zuwa cikin parlour'n hakan yasa itama Halwa tabi bayan ta, sai da suka zauna kafin Ummi tasake samun bakin magana

"Halwa ina kika shiga ne? Ina kika shiga kika bar mu cikin neman ki?" Tayi maganar tana dawo wa kusa da Halwan tare da riƙe mata hannu

Hawaye Halwa tasoma yi, cikin rawan baki tace "don Allah ku gafarce Ni Ummi nabi son Raina na tafi na barku amma bazan sake ba".

Washe baki Ummi tayi tana rungume ta cike da tsantsan murna, bakin ta sai faɗin "baki yi mana komi ba Halwa, baki yi mana komi ba wlh.."

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now