🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''.
*CHAPTER 31*
Lokacin da suka isa, gaba ɗaya haraban court ɗin cike yake da mutane, Khalil ce musu yayi "su shiga ciki". Don haka suka fice suka bar sa cikin motan yaɗau wayan sa yana neman layin Brr. Tahir.
*20 minutes*
Shigowan Alƙali yasaka kowa yayi shiru, duk kan su tashi sukayi har sai da Alƙali yazauna kafin kowa ma yazauna, daga nan Maga-takarda yamiƙe yasoma bayani kamar haka:
"Ayau 26 September 2020 zamu ci gaba da gabatar da shari'ar Alhaji Mubarak Mai kuɗi da Nazeefa Shehu".
Sannan yamiƙa takardun ga Alƙali, shi kuma ya'amsa yana gyara glass ɗin sa yasoma dubawa, sannan yaɗago kansa yana cewa
"Lauyoyi zaku iya farawa".
Khalil ne yatashi yasoma gabatar da kan sa
"Ni sunana '''BARRISTER IBRAHIM KHALIL ABDURRA'UF.''' lauya me kare wacce takawo ƙara, tare dani kuma akwai abokan aikina..".
"Brr. Tahir .A. Tahir". Cewar Brr. Tahir kenan da shima yatashi yagabatar da sunan shi
"Tare dani Brr. Bilkisu Ahmad Sofana".
Zama sukayi gaba ɗayan su.
"Ni kuma ni ne Brr. Mahmud Sudais, lauya me kare wanda ake ƙara, tare dani akwai..".
"Brr. Shamsudden Munir".
Su ma zama sukayi, Alƙali duƙar da kansa yayi yaɗan yi rubutu tukun yaɗago kai yana kallon su, hakan yasaka Brr. Khalil yamiƙe yasoma magana
"Ya me girma me Shari'a, ina son agabatar min da Nazeefa Shehu don in mata tambayoyi".
"Kotu ta baka dama". Alƙali yafaɗi hakan yana aje Bairo ɗin hannun sa
Maga-takarda yamiƙe yace "idan akwai Nazeefa Shehu anan tafito".
Nazeefa da jikin ta yayi mugun sanyi, gaba ɗaya sai taji cikin ta yasoma rugugu ƙafanta kuma sai faman rawa suke yi don bata taɓa tsayawa cikin taron mutane ba, Mom dake kusa da ita tace
"Tashi kije mana, ki cire tsoro aran ki kinji".
Gyaɗa kai kawai tayi taɗago tana kallon mutane nan idanun ta yafaɗa akan na Khalil, kafe ta da idanu yayi ko ƙiftawa baya yi hakan yasaka tamiƙe tafara nufo shi, tana isowa wani ɗan sanda yace tashiga nan". Babu musu kuwa tashiga tatsaya kanta a ƙasa, takowa Khalil yayi ya'iso gaban ta

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a