🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''*JIKAR LAWALI CE*✍️
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''.
*CHAPTER 43*
Ƙarfe 10:30pm. Su Khalil da Brr. Tahir tare da Sameer suka shigo gidan, daƙyar ma Khalil yayarda suka biyo shi don da yace "baya son rakiyan". Shi da kan sa yashiga har ɗakin ta yace "tafito parlour" daga haka yajuya yafita, ita kuma tamiƙe jiki a sanyaye tagyara mayafinta tafito, ahankali taƙarisa tazauna aƙasa tana gaishe su, cike da fara'a suka amsa sannan ne Sameer yasoma musu wa'azi cikin raha, daga ƙarshe suka yi musu fatan alkhairi tare da sanya alkhairi a auren nasu
Har bakin Gate Khalil yaraka su da zasu tafi, yadawo yatarda Saleema tana nan zaune inda take, be ce komi ba yanufi ɗakin sa, yana shiga yasoma cire babban rigan dake jikin sa bayan ya cire Hulan kansa, agogon hannun sa yacire tare da cire links ɗin rigan sa yazube su yanufi parlour
Har yanzu tana nan zaune inda take, zama yayi kan kujera yana kallon ta, sai kuma yaɗauke kai yana kallon ledan da suka shigo dashi, miƙewa yayi yanufi kichen sai gashi ya dawo da plate a hannu tare da wuƙa, zama yayi a ƙasa kamar yanda itama take zaune a ƙasan, yajawo ledan yabuɗe yaciro Kazan ciki yasoma yanka wa cikin plate ɗin don yayi daɗin ci, bayan ya gama duk yajera mata a gabanta da su Holandia sannan yakalle ta yace
"buɗe fuskar ki kici".
Ahankali tayaye gyalen daga kanta taɗago tana kallon sa sai kuma takalli abinda ke gabanta, cike da tsananin kunya tanoƙe ko motsi ta kasa yi, ganin haka yaja baya yana ɗaukan wayan sa yasoma latsawa yana cewa
"Ki ɗauka kici nace".
Wannan karon batayi musu ba ganin ya matsa can baya kuma hankalin sa baya kanta, hakan yasa tasoma ɗauka tana ci duk da dama tana jin yunwa amma baza ta iya buɗe ciki taci ba, kaɗan taci tacire hannun ta cikin sanyin murya tace
"Na gama".
Ɗago kai yayi yakalli plate ɗin sannan yasake maida kansa kan waya yace "ki ƙara".
Hannu tasaka taci gaba taci, bata daɗe ba tasake tsame hannun ta, wannan karon da yaɗago kai miƙewa yayi yaɗau komi yanufi kichen dashi, yana dawowa yace tataso su je ɗaki, miƙewa tayi tabi bayan sa, suna shiga yanuna mata Toilet tashiga tawanke hannu da bakinta tafito, yasake nuna mata kan gadon.. ta ko haye can lungu taƙudundune da gyalen ta
Shi kuwa Toilet yashiga yayi wanka yafito yashirya cikin kaya sannan yahayo kan gadon yakwanta, shiru sukayi ko wanne yana jin numfashin juna, can kamar amafarki tatsinkayi muryan sa
"Ya jikin naki?"
Cike da jindaɗi ta'amsa masa ganin yanda yadamu da ita sosai, daga haka basu sake yin magana ba har sanda Khalil yaji numfashin ta na fita da ƙarfi hakan yagane tayi barci, juyowa yayi setting ta duk da baya kallon fuskarta hakan be hana yaƙure ta da idanuwansa ba, shiru yayi yana tunani yana bin ta da kallo, abinda be taɓa faruwa dashi ba yau sai gashi zai kwana da mace

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a