chapter Twenty Two

99 7 9
                                    

🎓
🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuDahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

       *BOOK TWO*

.

_______________________________

        *CHAPTER Twenty Two*

________🎓Zaman Khalil da Halwa zama ne tamkar ba mata da miji ba, babu abinda ke haɗa su sai gaisuwa, idan yatafi aiki itama sai tatafi school ɗin ta

Zata gyara gidan tayi musu girki kullum bata gajiya amma magana wannan baya haɗa su in ba ya zama dole ba

A ɗan zaman nan da suka yi a matsayin ta na matar sa tuni ta gane ta afka ƙaunar sa, bata da aiki yanzu sai tunanin sa da kuma zaman da suka yi abaya lokacin yana mata magana sosai, karatun da yasaka ta a gaba da kuma soyayyar Khalil wanda bata san sanda tafaɗa ba sun haɗe mata sun yi mata yawa, don haka gaba ɗaya yanzu ta rame ko kaɗan bata da sukunin zuciyarta, ga karatu ga tunanin da yazamar mata jaraba, da farko ta so duk yanda za'a yi ta yakice sa a ranta amma ina hakan ya gagara, wani lokacin har zuwa take yi tazauna kusa dashi tana masa magana ko wai zai riƙa kulata tasamu sukunin zuciya sabida yanda ƙaunar sa ke azalzalan ta, amma yanda tazauna haka zata tashi babu abinda ke haɗa su, hakan na ƙara saka ta shiga mawuyacin hali, har tashiga ɗaki tayi ta kuka tana tirr da zuciyar ta akan rashin adalcin da tayi mata, duk a maza ta rasa wanda zata so sai mijin ƴar uwanta da take ganin ƙimar ta sosai, wanda idan ba ƙaddara da ya haɗa su ba ba ta tunanin zata iya auren sa, a yanda tafahimta Khalil bazai taɓa son ta ba Saleema kaɗai yake so, ita kawai zata yi zaman haƙuri ne har sanda Saleeman zata samu lafiya tasan makomar ta, tunda tarigada ta saka a ranta idan Saleema bata son auren to guduwa zata yi, wannan shine kaɗai hanyan da taga zata iya guje wa auren nan.


            *****
Ahmad na wajen Ummi har yanzu ita take kula dashi, idan tatafi aiki sai kuma Larai tahaɗa su ita da Husna taci gaba da kula dasu, idan kuma ta dawo sai tarage mata aiki wajen amsar Ahmad ɗin, tunda aiyukan sun yi ma Larai yawa, ga aikin gida ga kuma raino.

Har yanzu dai Saleema babu labarin ci gaba, kullum iyayen ta addu'a suke yin mata Allah yatashi kafaɗun ta, idan Ummi taje aiki wuni take yi a wajen ta tunda yanzu ana barin ta tana shiga

Itama Halwa wani lokacin tana zuwa duba ta, takan yi kuka duk sanda taje taga Saleema cikin wannan halin da ba ta sanin a duniyar da take ciki.

Rayuwa taci gaba da tafiya yanzu gashi har Saleema ta shafe wata biyu curr kafin tafarfaɗo, zo ku ga murna wajen ahalin ta duk da kuwa ba wai ta dawo hayyacin ta gaba ɗaya bane tana cikin ciwo sosai, amma dai ahaka kowa ke murna da samun lafiyan ta

An ci gaba da treating ɗin ta har zuwa ɗan wani satikai inda tasamu lafiya sosai alhmadulillah sai abinda ba'a rasa ba, ciwon zuciyarta yanzu shine matsalan ta, but duk da haka an ɗaura ta akan magani

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now