🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
*BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
♠️*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_*بسم الله الرحمن الرحيم*
⚖
*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''*JIKAR LAWALI CE*✍️ ~Wattspp Number 07065334256~
*Wattpad: UmmuƊahirah*👈
*\F.W.A📚/*
'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''.
*CHAPTER 33*
Halwa ce zaune saman gado kusa da na Saleema dake barci har yanzu bata farka ba, but yanzu babu Oxgyen da aka saka mata sabida Numfashin ta ya dai-daita
itama Halwan an sanya mata drip a hannun ta, Ummi dake zaune saman kujera tana yanka Lemo cikin plate, bayan ta gama sai taɓare ayaba shima duk tajera akan plate ɗin tamiƙa ma Halwa tace
"Riƙe kisha wannan nasan zai fi miki, bazaki zauna haka tun safe baki ci komi ba".
Babu musu Halwa ta'amsa tasoma ɗauka tana sha, Nurse ce tashigo da sallaman ta taƙariso wajen su tana cewa
"Ya jikin naki? Da fatan yanzu kina jin ƙarfi sosai ajikin ko?"
Gyaɗa kai Halwa tayi tana kallon ta
"Ok gashi wannan maganin ki ne zaki riƙa sha a rana sau biyu, Allah yasauwaƙe".
Ummi ne ta'amshi maganin tana cewa "Ameen mungode".
Matsowa tayi tagyara mata ruwan kafin tafito da allura cikin aljihun ta tasoma haɗawa tana faɗin
"Har yanzu ita bata farka bane?".
"Eh". Ummi ta'amsa mata tana kallon Saleema".
"Ok idan ta farka Sister Asma'u sai ki sanar da Doctor ɗin".
Ummi tace "ok ba matsala".
Alluran tatsira cikin Drip ɗin Halwa kana tayi musu sallama tafice, ruwa Ummi tamiƙo mata tare da ɓallo maganin shima tamiƙa mata tace
"Gashi kisha, amma kiyi sauri kishanye Fruits ɗin kinsan babu komi acikin ki".
Gyaɗa kanta tayi ta'amsa maganin tazuba a baki tana runtse idanu kafin takora da ruwa, daƙyar ta iya haɗiyewa tana sakin nishi, murmushi Ummi tayi tace
"Da alamu bakison magani ko?"
Itama Halwa murmushin tayi tana sauke kanta ƙasa
"To yi sauri kishanye mana".
Ci gaba tayi da shan Fuirts ɗin har tashanye, Ummi ta'amsa plate ɗin ta'ajiye, gyara zaman ta tayi tana kwanciya tare da rufe idanun ta, barci take ji sosai kasancewar Alluran da akayi mata cikin Drip ɗin na barci ne coz ana son tasamu hutu sosai, babu jimawa kuwa barci yayi awon gaba da ita, koda Ummi tayi magana taji shiru hakan yatabbatar mata da barci ya ɗauke ta, tashi tayi takoma saman kujerun dake ɗakin taɗau remote tana sauya tasha, a *ƳAN CI T.V* tabari tasoma kallon Labaran da ake nunawa na hukuncin da aka yanke akan su Alh. Mubarak, in banda girgiza kai babu abinda Ummi take yi.

YOU ARE READING
BARRISTER IBRAHIM KHALIL
RomanceLabarin wani matashi ne me farin jini da Sa'a, duk abinda yasaka a gaba to sai yasami Sa'a