Part 34

54 4 4
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

    *CHAPTER 34*

Kwance take saman gadon ta daga ita sai ƴar shimi fara ƙal, sai jan wando robber da yamatse ta sosai wanda da kaɗan yawuce gwiwarta, wayan ta dake ajiye saman gadon ne tasoma ringing sai tajawo tana kallon screan ɗin wayan, ganin sunan HONEY yafito ɓaro-ɓaro yasaka tayi peacking call ɗin tana kangawa a kunne, shiru tayi tana sauraron sa sai kuma ta'ajiye wayan tamiƙe tsaye tana ɗaukan Red colour Jaket ɗin dake ajiye saman gadon tasaka, Jaket ɗin irin me buɗaɗɗen gaba ne sai Belt da aka saka a iya tsakiya wajen cikin ta, iyakan cinyan ta yatsaya mata, sai taɗau Facing cap shima Red tasaka tafito, Ahmad ne kaɗai yake zaune Parlourn yana kallo takalle shi tace

"Idan Mami tafito kasanar mata nafita wajen Sharif".

Ahmad yace "ok".

Fita tayi tanufi inda yake tsaye jikin motan sa, tun fitowan ta yake kallon ta yana murmushi har ta'iso wajen

"My beautiful girl". Yace hakan yana sake faɗaɗa fara'ar sa

Ɗan cije laɓɓanta tayi tana kallon sa itama cikin murmushi tace "ya kake?"

"Lafiya, kefa?"

"Lafiya lau". Tayi maganar tana jingina da motar itama kamar yanda yayi, sai dai facing juna suke yi

"Kinsan me?".

Girgiza kanta tayi still tana kallon sa

"Kullum sai in riƙa jin ƙaunar ki na ƙara zauta Ni, har yanzu nakasa sabawa da yanayin da nake ji a kanki".

Sai ya ɗan yi murmushi yana shafa kwantaccen ƙasumban sa yaƙure ta da ido yace

"Na ƙosa Kausar kikasance mallakina, ina ji ajikina kamar in ban yi dagaske ba zan iya rasa ki".

Kallon da take masa ne yasauya zuwa mamaki, amma sai batace komi ba taɗauke kai tana jin zuciyar ta na bugawa, kiran sunan ta Sharif ɗin yayi, sai taɗago kai kawai tana kallon sa

Yace "har yanzu baki bani amsa ba akan maganar da mukayi dake".

"Wace magana kenan?" Tatambaye sa cike da rashin fahimta

Murmushi yayi yace "har kin manta maganar da mukayi lokacin da zamu dawo Nigeria? Haba Dear yakamata ki bama zance na muhimmanci, Ni nayi miki alƙawari wlh zan bar ki kici gaba da aikin ki koda munyi aure, be kamata mu zauna muna ɓata lokaci ba bayan kinsan da cewa mun fahimci juna, kuma iyayen mu sun san komi, to me muke jira?"

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now