Part 27

45 2 0
                                    

🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️🎗️
   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*
                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma'il*
_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*


*FEENAH WRITER'S ASSO📖*
'''®Ɗaya tamkar da Dubu💪✓'''

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*👈

         *\F.W.A📚/*

'''ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH
ALHAMDULILLAH'''
_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al'umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN 🤲 ya Allah._

*SADAUKARWA*
_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*
'''NAFEESAT
LABARIN DEEBIZAH
JARUMAI
RAYUWATA
NUSNIM
BUTULCI
SO MAI ZAFI.'''

.

     *CHAPTER 27*

     Tayi tafiyan da yakai kusan awanni biyu batare da ta gajiya ba, kuma bata da alaman tsayawa tafiyan kawai take yi but batasan inda take tsulmiya ƙafafuwan ta ba, har sai da taji ƙafafun nata sun soma nauyi suna takawa daƙyar kafin tasamu gefen wani shago tazauna tana sakin nishi, kallo ɗaya kayi mata zaka gane tana cikin wani mawuyacin hali da baza ka iya fassara shi ba, idanunta gaba ɗaya sun wani jeme sun yi luhu-luhu, har alokacin kuma basu gama washe wa daga canza kalan da suka yi ba, hannun ta tasanya tariƙe goshin ta tana runtse idanu, shiru tayi tana sauraron bugun zuciyarta da yanzu yaƙara hauhawa kamar zai faso ƙirjin ta sabida wani irin bugawa da yake yi

Takun takalmi taji da gudu-gudu, hakan yasaka tabuɗe idanun ta tasauke akan sa, shima ɗin itan yake kallo har ya'iso wajen ta, sai yashiga wani lungu da shaguna biyu suka rufe wajen, bata sauke idanun ta a wajen ba kuma bata motsa ba har sai da tajiyo takun wasu mutanen, hakan yasaka tajuya tana kallon su, mutane uku ne da baƙaƙen kaya sun sha Suit, hannun su na cikin rigan su da alamun dai akwai abinda suka ɓoye, har sun gibta ta sai ɗaya yadawo da baya yana kallon ta da fuskar shi a ɗaure yace

"Keee ƴan mata bakiga wani yawuce tanan ba? Ina kikaga yabi?"

Ɗauke idanun ta tayi akan sa tamayar inda taga mutumin nan ya ɓoye, sai taga yaleƙo kan sa suka sake haɗa idanu, kallon ta kawai yake yi da idanun sa masu bala'in kyawu ko ƙyaftawa baya yi batare da ko yayi mata alaman kar tatona shi ba

"Ke magana muke miki fa? Baki ga wani yawuce tanan ba?"

Gyaɗa kan ta kawai tayi tana sauke idanun ta ƙasa, wucewa sukayi batare da sun sake magana ba, sai da sukayi nisa da tafiya kafin yafito, ita kuma taɗago idanu tana kallon sa still shima kallon ta yake yi, sai da sukayi 2min suna kallon juna kafin yajuya dasauri yawuce, kau da kai tayi tana tunanin abinda yasaka mutanen suke neman sa? Sai kuma taruntse idanuwan ta tana jin damuwan ta na dawo mata, hawaye ne suka soma zuba cikin idanun suna gangarowa saman kuncin ta

"Ya zan yi?" Tafaɗa a fili tana wurwurga idanu a hanya

"Wayyo Allah Ni Halwa, Allah na roƙe ka Allah kakawo min agaji, Allah na roƙe ka ya Allah kataimake ni, kataimaki rayuwata, Allah ina buƙatan taimako". Sai tafashe da kuka me ban tausayi

Ɗaura kanta akan ƙafafunta tayi tasoma rerawa, kai daga jin kukan kasan na ƙunci da baƙin ciki ne, ta jima a wannan yanayin kafin tamiƙe tasoma tafiya, alokacin hankalin ta baya jikin ta tana can tana tunanin kalaman Nura tana yi tana sharan hawaye, sosai tadamu ƙwaƙwalwan ta da son sanin meyasaka ya'aikata mata hakan? sai jinta tayi a ƙasa batare da tasan abinda yasame ta ba

BARRISTER IBRAHIM KHALILWhere stories live. Discover now